Bayan 'yan sa’ao’i da sace wani dan majalisar dokokin jihar Katsina, wasu ’yan bindiga sun kai hari a kauyen Tafoki na karamar hukumar mulkin Faskari, inda suka yi awon gaba da kanwar mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar, Shehu Dalhatu Tafoki.