Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta tabbatar da kisan dan sanata Bala Na’Allah mai wakiltar mazabar Kebbi ta kudu, Kyaftin Abdulkarim Ibn Na’Allah.
Gwamna Simon Lalong na jihar filato ya sassauta dokar hana fita da ya saka a wasu sassa na jihar kamar garin Jos da Bassa sakamakon rikicin da ya barke a jihar da ya haifar da rashin tsaro.
Ma’aikacin gidan talabijan na Channels, Kayode Okikiolu, ya musanta labarin cewa hukumar tsaro ta farin kaya wato DSS ta kama shi da abokin aikinsa Chamberlain Usoh a ranar Alhamis.
Faifan Bidiyon Kayode Okikiolu
‘Yan bindigan da suka yi awun gaba da yaran islamiyyar ta garin Tegina dai sun rike yara a tsawon kwanaki 88 kafin suka sako su da maraicen jiya Alhamis.
Wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya yi nuni da cewa gwamnati na yin wani shiri cikin sirri mai taken Sulhu, wanda aka tsara don fitar da kwamandojin kungiyoyin 'yan ta'adda, da suka hada da Boko Haram da ISWAP daga cikin dazuzzuka, gyara su da samar musu da sabbin hanyoyin rayuwa.
Gabanin babban taron jam’iyyar PDP, rikicin cikin gida na kara tsananta a cikin jam'iyyar a yayin da shugaban jam’iyyar Uche Secondus ya yi kememe cewa ba zai bar kujerarsa ba har sai ya kamalla wa’adinsa na shekara 4.
Shugaban jam’iyyar PDP Uche Secondus ya yi ganawar sirri da tsohon shugaban Najeriya, Cif Olusegun Obasanjo a Abeokuta ta jihar Ogun, a bisa dalilin neman bakin zare warware rikicin cikin gida da ya dabaibaye jam’iyyarsa ta PDP.
Shugaban Najeriya Muhammafu Buhari ya lashi takobin cewa ba zai sauka daga kan kujerar shugabanacin kasar ba har sai ya kawo muhimman sauye-sauye da zasu kawo ci gaba.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya tura tawagar da ta kunshi muhimman mukarrabansa a fadar sarkin Bichi da ke jihar Kano don ta wakilce shi a bukin daurin auren dansa Yusuf Buhari, da za a yi a yau Juma’a a garin Bichi.
Tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa karkashin tutar jam’iyyar PDP, sanata Ibrahim Mantu ya rasu bayan fama da rashin lafiya.
Wasu daga cikin matafiya da suka tsira da ransu a harin da wasu mazauna garin Jos ta jihar Filato suka kai musu, sun ce wasu masu tausayi a cikin al'ummar ne suka taimaka musu suka sami tsira da ran su a wannan harin.
Majiyoyi daga jihar Zamfara sun bayyana cewa jumlar wadanda suka rasa ransu a harin a halin yanzu ya kai hudu a yayin da mutane 19 suke hannun 'yan bindigar.
Tsohon ministan matasa da wasanni a Najeriya, Solomon Dalung ya zargi wasu mukarraban shugaba muhammadu Buhari da yin katutu wajen hana mutane masu kyakyawar niyyar fadin gaskiya kan yanayin da kasa ke ciki ganinsa.
Wani Jigo a jam’iyyar PDP Cif Raymond Dokpesi, ya bayyana cewa jam'iyyarsa na da kyakkyawar damar sake karbe madafun iko a Najeriya ne kawai idan ta tsayar da dan takarar shugaban kasa daga Arewa a shekarar 2023.
Babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta shigar da karar jam’iyyar APC mai mulki da Mai Mala Buni a gaban kotu, tana neman a ta cire shi daga kujerarsa ta gwamnan jihar Yobe.
Wannan ya biyo ne bayan sanarwar da gwamnatin Najeriya ta fitar a makon da ya gabata, inda ta ce karin na daga cikin matakan samun ci gaba ta fannin samun kudaden shiga ga kasar.
A daidai lokacin da matsalolin tsaro ke kara ta’azzara, gwamna Bello Matawalle na Jihar Zamfara ya yi kira ga sauran takwarorinsa na arewacin Najeriya da ma gwamnatin tarayyar su hada gwiwa wajen samo mafita mai dorewa.
Rundunar sojin Najeriya ta bayyana cewa dakarun ko-ta-kwanan ta na runduna ta 25 sun sami nasarar dakile wani harin da aka yi yunkurin kaiwa a garin Damboa dake jihar Borno a safiyar Litinin.
Ana sa ran fitaccen dan wasan kwallon kafa Lionel Messi, ya isa birnin Paris na kasar Faransa a yau Litini don kammala shirye-shiryen komawa kungiyar PSG biyo bayan raba gari da Barcelona da ya bugawa wasanni a tsawon shekara 21.
Domin Kari