A ranar Talata ne Najeriya ta kara wa ma’aikatan gwamnati albashi da kashi 25% zuwa 35%, tun daga watan Janairu da ya gabata, in ji hukumar albashi, yayin da kasar mai mafi girman tattalin arziki a Afirka ke fama da matsalar tsadar rayuwa na kusan shekaru talatin.