Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dan Kunar Bakin Wake Ya Kashe Mutane Shida A Pakistan


Jami'an Kidaya aka auna a harin da a aka kai birnin Lahore a lokacin da suke cikin motarsu, a cewar hukumomin Pakistan.

Wani dan kunar bakin wake ya kashe akalla mutane 6 a gabashin Pakistan, ciki har da sojoji.

Hukumomi sun ce an auna wata mota ne dauke da jami’an kidaya a Lahore, babban birnin lardin Punjab mai mafi yawan jama’a a kasar, a harin da aka kai yau Laraba.

Hoton bidiyo da aka dauka ya nuna motar da aka ratattaka da kuma barnar da harin ya haddasa kan wasu babura.

‘Yan kungiyar Taliban dake Pakistan sun dauki alhakin kai mummunan harin wanda ya raunata kusan mutane 20.

Ministan lafiyar lardin, Khawaja Imran Nazir, ya ce 3 daga cikin mutanen na cikin mawuyacin hali.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG