A yau Talata ake sa ran Shugaban Amurka Joe Biden zai sanar da wani gagarumin sabon shirin da zai kawar da barazanar mayar da dubban mutanen da suka auri yan kasar Amurka zuwa gida.
An tuhumi wani dan jihar Arizona bisa laifuka hudu da suka shafi safarar bindigogi bayan da masu gabatar da kara na gwamnatin tarayya suka ce wani samame da aka gudanar a boye ya nuna cewa ya shirya kashe bakaken fata a wani harin da ya ke da nufin gudanarwa, a cewar tuhumar.
Shugaban Amurka Joe Biden da shugaban Ukraine Volodymyr Zelenskyy za su rattaba hannu kan wata yarjejeniyar tsaro ranar Alhamis, yayin da za su gana a Italiya a gefen taron kolin kungiyar kasashe bakwai masu karfin tattalin arziki a duniya.
Ambaliyar ruwa da guguwa mai karfi sun shafi sassan kudancin jihar Florida da yawa a ranar Laraba, lamarin da ya sa hanyoyi suka cika da ruwa, abinda ya kawo cikas ga ‘yan wasan kwallon hockey na Florida Panthers da ke kan hanyar zuwa gasar cin kofin Stanley da za a yi a Canada.
An kama wasu mutane takwas daga kasar Tajikistan da ake zargin suna da alaka da kungiyar IS a Amurka a cikin 'yan kwanakin nan, a cewar wasu da ke da masaniya kan lamarin.
Wasu jami’an Amurka biyu sun ce shugaba Joe Biden ne ya amince da matakin tura makaman.
A yau Talata ne babban jami'in Hamas, Sami Abu Zuhri, da ke wajen Gaza ya ce ta amince da kudurin tsagaita bude wuta kuma a shirye take ta tattauna kan cikakkun bayanai.
Ana kyautata zaton cewa sakataren harkokin wajen Amurka, Anthony Blinken zai gana da shugabanni a Misra da Isra'ila yau Litinin da zumar cimma nasarar dakatar da fadan.
A lokacin da shugaba Biden ya fito fili ya bayyana kudurin tsagaita bude wuta a Gaza, da Isra'ila da Amurka suka shirya kuma suka aikewa kungiyar Hamas, ya bayyana hakan ne ba tare da neman amincewar Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ba, in ji wasu jami'an Amurka uku masu masaniya kan lamarin
Dokar za ta hana jami’an kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa shiga kasar Amurka, za ta kuma soke bizarsu da kuma hana duk wani cinikin kadarorin da ke Amurka.
Shugaba Joe Biden, wanda ke kara sukar yadda Isira’ila ke yaki da mayakan Hamas a Gaza da kuma yawan mutuwar Falsadinawa, a wata sabuwar hira da aka yi da shi
Shugaban Amurka Joe Biden ya sanya hannu a wasu tsauraran matakan hana karban ‘yan ci rani masu neman mafaka da suke shiga Amurka ta iyakar kasar da Mexico ba bisa ka’ida ba, a wani babban mataki yayin da zaben shugaban kasa na watan Nuwamba ke karatowa.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.