Tsohon sanatan Amurka kuma wanda jam’iyyar Democrats ta amince ya tsaya takarar mataimakin shugaban kasa karkashinta, Joe Liebeman, ya riga mu gidan gaskiya yana mai shekaru 82 a duniya bayan da ya sha fama da wani rauni sakamakon wata faduwa da ya yi, kamar yadda danginsa su ka fada jiya Laraba.
Jiya Laraba, masu bincike sun fara tattara abubuwan kafa shaida daga cikin jirgin ruwan da ya hankade wani sashin gadar Francis Scott a ranar Talata.
Sama da mako guda bayan da hukumomin jamhuriyar Nijar suka bada sanarwar yanke huldar ayyukan soja da Amurka gwamnatin Amurkar ta ce ta yi na’am da wannan mataki saboda haka nan gaba kadan kasashen biyu zasu tattauna kan hanyoyi mafi amfani wajen kwashe sojojin Amurkan daga kasar.
Ana ci gaba da ƙoƙarin ayyukan ceto akan gadar Baltimore da ta rugurguje, inda masu aikin ceto a karkashin teku suka koma wurin da sanyin safiyar yau Laraba bayan rashin nasara saboda hazo cikin dare
Gwamnan Jihar Maryland, Wes Moore, ya kore yiyuwar harin ta'addanci sakamakon rugujewar wata muhimmiyar gada a birnin Baltimore da safiyar yau talata bayan da wani jirgin ruwan dakon ya afka mata.
Shugaban kasar Amurka, Joe Biden ya ayyana rugujewar gadar Baltimore a matsayin mumunar hatsari inda ya yi alkawarin sake gina babbar tashar jiragen ruwa dake gabashin kasar nan take bayan wata jirgin ruwa ta ci karo da gada
Dangantaka tsakanin Shugaba Joe Biden da Fira Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ta fara yin tsami ne a Litinin bayan da Amurka ta amince da kudirin tsagaita wuta a Gaza a taron Majalisar Dinkin Duniya tare da kakkausar suka daga Shugaban na Isra'ila.
Wani jirgin ruwan mai dakon kwantena ya kutsa cikin wata babbar gada da ke Baltimore a jihar Maryland da sanyin safiyar Talata, lamarin da ya yi sanadin karyewarta a wasu wurare tare da nutsewa cikin kogi.
Wata budurwa ta harbe kanta har lahira da wata bindiga mallakin maitaimakin babban sufeton ‘yan sanda a harabar wani ofishin ‘yan sanda da ke California, a cewar hukumomi a ranar Litinin.
Likitoci a birnin Boston na jihar Massachusetts da ke Amurka sun ce sun yi nasarar aikin dashen kodar alade da aka canzawa kwayoyin halitta a jikin wani mutum majinyaci mai shekaru 62 da ke da ciwon koda a mataki mai muni.
Idan har Majalisar Dattawa ta ki amincewa da kudurin kasafin kudin, babu makawa sai an rufe wasu ma’aikatun gwamnatin kasar.
A ranar Juma'a ne Rasha da China suka ki amincewa da wani kuduri na Majalisar Dinkin Duniya da Amurka ta yi kira da a gaggauta tsagaita wuta a yakin Isra'ila da Hamas a Gaza don kare fararen hula da ba da damar kai agajin jin kai ga Falasdinawa sama da miliyan biyu da ke fama da yunwa
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.