Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken a Litinin din nan ya yi alkawarin karin dala miliyan 133 don tallafawa kasar Haiti, yana mai cewa, rikicin da ke kara kamari ya nuna butar gaggawa na tura dakaru na kasa da kasa.
An fara bikin Oscars na 2024 da Da'Vine Joy Randolph, wadda ta lashe lambar yabo ta farko a daren. Dama an yi hasashen za ta samu lambar yabon.
Shugaban Amurka, Joe Biden ya bude jawabinsa na shekara-shekara tare da sukar Trump kai tsaye kan gayyatar Shugaban Rasha Vladimir Putin da ya kai wa sauran kasashen kungiyar NATO hari idan ba su kashe kudi mai yawa kan tsaro ba.
'Yar Majalisar dattijan daga Alabama, Katie Britt, wadda ita ce 'yar jam'iyyar Republican mafi karancin shekaru da aka zaba a Majalisar dattijan Amurka, ta soki Shugaba Joe Biden da gwamnatinsa kan iyakoki, yanayin tattalin arzikin Amurka da batutuwan da suka shafi laifuffuka da tsaro a matsayin martani.
An gurfanar da wani fitaccen malami kuma mai fafutuka ‘dan kasar Sudan ta Kudu da ke gudun hijira a Amurka a jihar Arizona tare da wani dan kasar Utah da aka haifa a kasar Sudan ta Kudu bisa zargin saya da fitar da makamai na miliyoyin daloli domin kokarin kifar da gwamnatin kasarsu.
Miliyoyin Amurkawa a jihohi 15 da tsibirin Samoa na Amurka ne ke kada kuri'a a yau Talata, rana mafi girma ta kada kuri'a a zaben 'yan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Democrat da Republican.
Kamala Harris ta ce ya kamata kungiyar Hamas ta amince da yarjejeniyar tsagaita wutan, ta kuma yi kira ga gwamnatin Firai Minista Benjamin Netanyahu da ta dauki matakin kara kai agaji a Gaza.
Akalla Falasdinawa 104 ne aka kashe a birnin Gaza ranar Alhamis yayin da sojojin Isra’ila suka bude wuta kan mutanen da ke kokarin samun abinci daga manyan motocin jin kai.
Shugaban Amurka Joe Biden da tsohon shugaban kasar Donald Trump sun lashe zaben fidda gwani na jam'iyyarsu a jihar Michigan ranar Talata.
Makarantar koyon aikin likita a birnin New York za ta zama kyauta ga duk ɗalibai daga yanzu saboda gudummawar dala biliyan 1 daga wata tsohuwar farfesa, gwauruwar wani mai saka hannun jari na Berkshire Hathaway.
Shugaban Amurka Joe Biden da tsohon shugaban kasar Donald Trump za su nufi kan iyakar Amurka da Mexico a cikin wannan mako, inda za su maida hankali kan daukar matakan gaggawa dangane da cigaba da kwararar dubun dubatan bakin haure da ke ke shigowa Amurka.
Firai Ministan Isra'ila ya fada a ranar Lahadi cewa, yuwuwar tsagaita wuta a yakin da kasarsa ke yi da mayakan Hamas zai jinkirta kai hari ta kasa ne kawai a birnin Rafah da ke kudancin Gaza, inda ya zama mafaka ga fiye da rabin al'ummar yankin da ke fuskantar rikici.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.