Daraktan Hukumar Binciken Manyan Laifuka ta Amurka FBI, Christopher Wray, ya ce Hukumar FBI na gudanar da bincike kan gudanar da “ofishin ‘yan sanda” ba bisa ka’ida ba da kasar China ke yi a New York na Amurka.
A daren jiya tsohon shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana aniyarsa ta sake shiga takarar shugaban kasa a shekarar 2024, mako guda bayan da jami’iyarsa ta rage karfi a majalisar dokokin kasar a zaben rabin wa’adi da aka gudanar a makon jiya.
Makomar manufofin shugaban Amurka Joe Biden a sauran shekaru biyu da suka rage a wa’adinsa sun rataya ne kan jam'iyyar da ta samu rinjaye a majalisar dokokin Amurka, yayin da kasar ke dakon sakamakon zaben rabin wa’adin da aka yi ranar Talata.
Amurkawa sun kada kuri'a a zaben rabin wa'adi na farko karkashin shugabancin Joe Biden, inda ake sa ido sosai kan yadda zaben sai tabbar da jam'iyar da ke da iko a Majalisa, kujerun gwamnoni da sauran manyan zabuka.
Wasu daga cikin ‘yan takarar da ke neman kujerun majalisar karkashin jam’iyyar Republican, sun fi karkata hankulansu ne kan yadda sahihancin zaben zai kasance, inda suke ta nanata ikirarin tsohon shugaban kasa Donald Trump, wanda ba tare da wata hujja ba, yake cewa an tafka magudi a zaben 2020.
An sami karin Amurkawa 'yan asalin Najeriya da suka tsaya takara a zaben wa'adin rabin lokaci da za a gudanar gobe a Amurka.
Taylor Swift ta kafa tarihi a matsayin mawakiyar farko da ta taba samun wakokinta goma suka shiga jerin manyan wakokin 100 da aka fi so a cikin mako guda da faifan ta mai suna "Midnights."
Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ce za ta kwashe jami'an diflomasiyyarta da aikinsu bai zama wajibi ba daga birnin Abuja sakamakon barazanar tsaro da birnin ke fuskanta.
Gwajin asali na kwanan nan da Meghan Markle ta yi ya nuna cewa kashi 43 cikin 100 na asalinta ‘yar Najeriya." Ta bayyana hakan ne a wani sabon shafi na faifan asali na wani shafin sada zumunta Spotify, da ake kira Archetypes.
Trump da magoya bayansa sun yi watsi da wannan bincike da kwamitin ke gudanarwa, wanda suka kwatanta a matsayin bi-ta-da-kullin siyasa.
Tsohon shugaban kasar Amurka Donald Trump ya kai karar gidan talabijin na CNN bisa zargin bata masa suna, ya kuma nemi a biya shi diyyar fiye da dala 75,000 da kuma diyya ta dala miliyan 475, a cewar wata karar da aka shigar a yau litinin, kamar yadda CNN ta rawaito.
Mazauna jihar Florida sama da miliyan biyu ne hukumomi suka ba umarnin su bar gidajensu yayin da guguwar Ian ke kusantar yankin.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.