An sami karin Amurkawa 'yan asalin Najeriya da suka tsaya takara a zaben wa'adin rabin lokaci da za a gudanar gobe a Amurka.
Taylor Swift ta kafa tarihi a matsayin mawakiyar farko da ta taba samun wakokinta goma suka shiga jerin manyan wakokin 100 da aka fi so a cikin mako guda da faifan ta mai suna "Midnights."
Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ce za ta kwashe jami'an diflomasiyyarta da aikinsu bai zama wajibi ba daga birnin Abuja sakamakon barazanar tsaro da birnin ke fuskanta.
Gwajin asali na kwanan nan da Meghan Markle ta yi ya nuna cewa kashi 43 cikin 100 na asalinta ‘yar Najeriya." Ta bayyana hakan ne a wani sabon shafi na faifan asali na wani shafin sada zumunta Spotify, da ake kira Archetypes.
Trump da magoya bayansa sun yi watsi da wannan bincike da kwamitin ke gudanarwa, wanda suka kwatanta a matsayin bi-ta-da-kullin siyasa.
Tsohon shugaban kasar Amurka Donald Trump ya kai karar gidan talabijin na CNN bisa zargin bata masa suna, ya kuma nemi a biya shi diyyar fiye da dala 75,000 da kuma diyya ta dala miliyan 475, a cewar wata karar da aka shigar a yau litinin, kamar yadda CNN ta rawaito.
Mazauna jihar Florida sama da miliyan biyu ne hukumomi suka ba umarnin su bar gidajensu yayin da guguwar Ian ke kusantar yankin.
Hukumomin Amurka sun kwashe shekaru suna son a dawo da shi Amurka domin fuskantar shari’a kan laifukan leken asiri.
Hukumar NDLEA mai yaki da safaran miyagun kwayoyi ta Najeriua ta kama wasu masu safaran muggan kwayoyi da hodar iblis ko cocaine da yawansa ya kai na tan 1.8, ko kwatankwacin kilogram 1855 a birnin Lagos.
Guguwar Fiona ta afkawa gabar tekun Puerto Rico da ke kudu maso yamma a ranar Lahadi yayin da ta haifar da zabtarewar kasa, ta kuma kifar da na'urar wutar lantarki sannan ta tsaga kwalta.
Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta karrama Deborah Samuel dalibar da ta gamu da ajalinta a kwalijin ilimi ta Shehu Shagari da ke Sokoto a hannun wadansu masu tsattsauran ra’ayi.
Mako guda kafin wa’adin tsohon shugaban Amurka Donald Trump ya kare a watan Janairun bara, ‘yan jam’iyyar Republican 10 a majalisar wakilai sun bi sahun gaba daya ‘yan Democrat wajen kada kuri’ar tsige shi saboda tada tarzoma da aka yi a ranar 6 ga watan Janairu a ginin majalisar dokokin Amurka.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.