Wata shararriyar mawakiyar Amurka Mary Wilson da tayi fice a cikin fitattun mata mawaka uku da ake kira da The Supremes a cikin shekarun 1960 ta mutu tana da shekaru 76.
Gabanin babban taron Tarayyar Afirka, shugaban Amurka Joe Biden ya ce gwamnatin kasar ta dukufa wajen aiki tare da Tarayyar Afirka domin cimma manufofinsu na samun kyakkyawar rayuwa da makoma.
Yau za'a fara sauraron karar sake tsige tsohon shugaban Amurka Donald Trump a majalisar dattawan Amurka.
Shugaban Amurka Joe Biden, ya ce ba zai dage takunkumin tattalin arziki da aka kakabawa kasar Iran ba, har sai Tehran din ta rage yawan aikin bunkasa sanadarin Uranium din ta, kamar yadda aka cimma, a yarjejeniyar kasa-da-kasa ta 2015, wanda aka yi, don hanata hada makaman, na kare dagi.
A yau Lahadi shugaban addini a Iran Ayatollah Ali Khamenei ya yi kira ga Amurka da ta dage duk wasu takunkumai a ka Iran indai har Washington na son Tehran ta ruguza shirinta na kera makaman nukiliya.
Shugaban Amurka Joe Biden, ya yi alkawarin cewa Amurka za ta yi matukar dada taka rawa a harkokin duniya a tsawon wa'adinsa, ya na mai kawo karshen abin da ya kira "shekaru hudu na yin watsi da kuma amfani da harkokin waje ba bisa ka'ida ba" da tsohon Shugaba Donald Trump ya yi.
Majalisar dattawan Amurka zata fara shari’a mai cike da tarihi ta tsige tsohon shugaban Amurka Donald Trump a wannan wata, inda zata kammala da kada kuri’a da zata yanke hukumci a kan ko yana da alhakin ingiza tarzoma a kan majalisar dokoki a ranar 6 ga Janairu.
Shugaban Amurka Joe Biden na shirin karbar bakuncin wasu sanatoci 10 ‘yan jam’iyyar Republican don tattaunawa yau Litinin game da wani sabon zagaye tallafin tattalin arzikin coronavirus.
Lauyoyin tsohon shugaban sun kasa cimma matsaya akan dabarar da ta fi dacewa don kare shi a majalisar dattawan kasar.
Cibiyar yaki da cututtuka masu yado ta Amurka ta CDC ta fitar da wani umarnin gama-gari da yammacin ranar Juma’a na tilasta saka kyallen rufe huska a cikin kowane nau’in sufurin jama’a da zai fara aiki cikin daren gobe Litinin, yayin da kasar ke kara samun dubban mace mace.
Gwamnatin sabon shugaban Amurka Joe Biden zata dakatar da tsarin banbance tsakani sha’anin cikin gida da na kasashen waje da aka saba da shi a Amurka, wurin tinkarar batutuwan barazana ga tsaron kasa.
A karon farko tun bayan da aka rantsar da shi, shugaban Amurka Joe Biden ya yi magana da shugaban Rasha Vladimir Putin, inda ya bayyana damuwar Amurka kan wasu batutuwa.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.