A jawabinsa yayin karo na 30 na taron kolin Najeriya a kan tattalin arziki daya gudana a Abuja, Ministan Kasafi Da Tsare-Tsare, Atiku Bagudu, ya baiwa ‘yan Najeriya tabbacin cewa duk da halin matsin da ake fama da shi a kasar, akwai fatan samun sauki a nan gaba.