Mataimakin Shugaban kasar Ghana, Dokta Mahamudu Bawumia, ya yi alkawarin zai kawar da wasu nau’oin haraji da gwamnati mai ci ta aiwatar, musamman harajin hada-hadar kudi na lantarki (E-Levy), idan aka zabe shi Shugaban kasa a babban zaben kasa mai zuwa.