Lamarin ya faru ne da misalin karfe 10 da minti 40 na safiyar Litinin 26 ga watan Disambar 2022.
Hukumar kula da fiton kayakin ‘yan kasuwar Nijar daga tashoshin jiragen ruwa zuwa sassan kasar CNUT ta kaddamar da ayyukan fadakarwa domin ganar da manyan ‘yan kasuwar dake oda daga kasashen waje.
Hukumar kula da fitar da kayayakin ‘yan kasuwar Nijer a tashoshin jiragen ruwa, CNUT, ta kaddamar da aiyukan fadakarwa don kaucewa matsalolin kan hanya a wannan lokaci da yakin Russia a Ukraine ke haddasa tsaiko ga harkar sufuri.
Hukumar kare hakkin dan adam ta CNDH ta gabatar wa Majalissar dokokin kasa rahotonta na shekarar 2021 wanda ke fayyace abubuwan da suka wakana masu nasaba da tauye hakkin bil adama a kasar ta Nijer a tsawon shekarar da ta shige.
Yayin da makamashi ke dada tsada a Janhuriyar Nijar, 'yan raji sun yi kira ga mahukunta da su rage ma talaka farashin makamashi.
Hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta Jamhuriyar Nijar, OCRTIS, ta kama wasu yan Najeriya da su ka hadiye miyagun kwayoyi da nufin safararsu zuwa kasar Aljeriya.
Jiya lahadi 18 ga watan Disamban 2022 aka yi hidimomin tunawa da ranar da Nijer ta zama Jamhuriya bayan zaben raba gardamar 1958 da ya fayyace a fili cewa jama’a na bukatar ganin kasar ta sami ‘yancin kai daga turawan mulkin mallaka.
Masu rajin kare dimokradiya a jamhuriyar Nijer sun yi na’am da taron da ake shirin farawa a yau Talata 13 ga watan disamba a nan birnin Washington DC a tsakanin kasar Amurka da kasashen nahiyar Afirka.
Yayin da talakawa ke ci gaba da fama da matsalar ruwan sha a Janhuriyar Nijar, masu ruwa da tsaki sun tashi haikan wajen kokarin hada karfi da karfe don magance matsalar.
Wannan na zuwa ne bayan la’akkari da barazanar lalacewar tarbiyar da ake fuskanta a wannan lokaci da kafafen sada zumunta ke zama wani bangare na rayuwar al’ummar kasar.
An tarawa gwamnatin Jamhuriyar Nijar sama da biliyan 45 na euro don gudanar da ayyuakan jama’a har zuwa shekarar 2026.
A cigaba da samun nasara, da wani sa'in akan yi a yaki da ta'addanci, wasu gwamman masu aikata manyan laifuka da makami sun tuba a Janhuriyar Nijar.
A jamhuriyar Nijer wani harin ta’addanci da aka kai a tashar bincike ta ‘yan sandan garin Say dake a km 60 da birnin Yamai ya haddasa asarar rayukan da suka hada da jami’an tsaro da farar hula.
Wasu mutanen da ba a san ko su waye ba sun yi rubuce rubucen da jan fenti akan allunan shaidar titin shugaba Muhammadu Buhari dake birnin Yamai na jamhuriyar Nijar.
A Duniyar wakar Hausa da Janhuriyar Nijar an yi wani babban rashi bayan da shahararriyar mawakiyar nan mai suna Hafsou Garba ta rasu yau.
Hukumomin Nijar sun gudanar da wani taron hadin gwiwa da jakadun MDD da na kungiyar EU da nufin jan ra’ayin masu hannu da shuni akan bukatar samun gudunmowarsu a yunkurin tsarin ciyar da yara a makarantun boko.
Majalisar dokokin Nijar ta yi na’am da kasafin kudaden shekarar 2023 da nufin bai wa gwamnatin kasar cikakkiyar damar gudanar da ayyukan da ta kira na inganta rayuwar al’umma, sai dai ‘yan adawa a majalisar sun juya wa kasafin baya saboda a cewarsu ba a yi la’akkari da halin da kasar ke ciki ba.
Domin Kari