'Yar majalisar ta na kuma neman hukumar tara harajin Amurka ta bayyana harajin 'Yan takara.
Kalubalen siyasar shugaban Amurka Donald Trump ya karu yau Talata bayan da tsohon manajan yakin neman zaben sa, Paul Manafort ke fuskantar hukuncin zuwa gidan yari.
'Yan Jam'iyyar Republican na nuna damuwa akan ra'ayoyin jama'a game da farin jinin shugaban Amurka Donald Trump.
Mayakan kungiyar Taliban dake Afghanistan sun ce ba su suka kai hare hare a Kabul ba.
Hukumomin kiwon lafiyar al’ummar a Janhuriyar Nijer sun bada sanarwar mutuwar mutane 26 daga cikin mutane kusan 1500 da suka kamu da cutar amai da gudawa a gundumar Madarunfa dake yankin Maradi.
Majalisar Dokokin jihar Neja a Nigeria ta kori daya daga cikin mambobinta, Hon. Danladi Iya, mai Wakiltar karamar Hukumar Tafa.
A yayinda bukukuwan salla ke gabatawo, hukumar kiyaye hadurra ta Najeriya da ake kira FRSC a takaice ta tura jami'ai 35,000 don kula da manyan hanyoyin kasar mussamman a lokacin bikin sallah da za a yi ranar Talata mai zuwa.
Yanzu haka al’ummomin da suka koma yankunansu da aka kwato daga hannun mayakan Boko Haram a arewa maso gabashin Najeriya na kokawa game da batun rashin sabunta katunan zabensu.
Komi ya tsaya cik a kasar Zimbabwe yayinda ake jiran hukumcin kotu akan zaben shugaban kasar da aka gudanar a watan da ya gabata, wanda shine karon farko ba tare da tsohon shugaba Robert Mugabe ba.
Mayakan Taliban sun kwace wani sansanin sojoji a arewacin Afghanistan sun kuma kashe sojoji dayawa tareda yin awon gaba da wasu.
‘Yan sanda a birnin London sun ce wani mutum ya afka cikin wani gungun masu tafiya da kafa da mota kafin ya banke wasu shingaye dake wajen ginin majalisar dokokin Burtaniyya yau Talata, wasu mutane sun jikkata sakamakon hakan.
Manoma Tumatir a Najeriya sun ce hukumar kwastam da takwararta ta NAFDAC mai kula da harkokin ingancin abinci da magunguna ta kasa, sun sa sun yi asarar kimanin Naira Miliyan dubu goma a kakar noman tumatir ta bana.
A Najeriya masu fashin bakin al’amurran yau da kullum sun suna ci gaba da bada fassarar da bamdabam dangane da batun toshe kofar shiga majalisar dattawa da jami’an tsaro su kayi, wanda ya janyo korar babban darektan hukumar tsaron farin kaya na kasar Lawal Daura.
A karshen makon jiya ne hukumar UNDP tare da hadin gwiwa da gwamnatin kasar Japan suka kaddamar da shirin bada kayan noma kyauta ga mazauna kauyen Loko, na karamar hukumar Song a jihar Adamawa.
Cikin fursunoni 800 da aka yiwa afuwa har da matar tsohon shugaban Ivory Coast Simone Gbagbo.
Ma'aikatar kiyaye gobara ta jihar California ta ce ta yiwu a iya shawo kan gobarar dajin a cikin mako mai zuwa.
Fadar ta shugaban Najeriya ta nesanta Shugaba Buhari da alhakin tura kudurin doka na rage ‘yancin yada labarai wanda ya sami karatu na biyu a gaban majalisar dattawan kasar.
Yanzu haka wannan tafiyar ta janyo cece-ku-ce tsakanin ‘yan siyasar kasar dake zargin cewa batun lafiya ne zai kai shugaba Buhari Ingila.
Domin Kari