A cikin ‘yan kwanakin nan rahotanni na nuna cewa mayakan kungiyar Boko Haram suna sauya salon kai hare-harensu ciki har da kisan dauki daidai, da kuma na sari-ka-noke, da kona kauyuka ko kuma dasa bama bamai a gonaki.
Wasu jihohi 8, da birnin Washington a gundumar Columbia sun kai karar gwamnatin shugaba Donald Trump akan ba wani dan jihar Texas damar raba ka’idodin yadda za a yi wata irin bindiga mai amfani da na’urar 3D.
Shugaba Trump ya ce yana iya dakatar da ayyukan kasarsa idan bai sami amincewar gina ganuwa tsakanin Mexico kasar sa ba.
Jiya litinin Shugaban Amurka Donald Trump yayi wani cikakken bayani da bai taba yi ba a baya cewa, a shirye yake yayi ganawar kai-tsaye da Iran.
Yanzu haka ‘yan kasar Zimbabwe na dakon sakamakon muhimmin zaben da aka yi a kasar, wanda wasu dayawa ke fatan ta yiwu, ya kawo sauyi ga tattalin arzikin kasar da ke fuskantar koma baya bayan mulkin tsohon shugaban kasa Robert Mugabe mai tsauri da yayi na tsawon shekaru 38.
A Jamhuriyar Nijer, jarabawar ajin karshe a makarantun share fagen shiga jami’a da aka gudanar a tsakiyar watan nan na Yuli ta bar baya da kura bayan da wata cibiyar jarabawa ta bayyana sunan wani dalibin da ya rasu a jerin wadanda suka yi nasara.
Sama da gidaje 200 ne suka lalace sanadiyyar ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka yi a karamar hukumar Maru dake jihar Zamfara.
Manoman shinkafa a jihohin Kano, Jigawa da Katsina sun koka game da tsarin bada lamunin kayan noma karkashin shirin gwamnatin tarayya na tallafawa masu noman karkashin kulawar babban bankin kasar.
Direbobin tasi guda 11 sun mutu, wasu su su 4 kuma sun sami munanan raunuka a lokacin da wasu ‘yan bindiga suka budewa motarsu wuta a Afrika ta kudu.
Sakataren ma'aikatar harkokin wajen Amurka Mike Pompeo ya ce gwamnatin Iran ta zama alakakai ga al’ummar ta, ya kara da cewa Amurka bata tsoron ta kaiwa gwamnatin kasar farmaki a matakin koli yayinda Amurka din ke yin kira ga dukan abokan kawancenta su hada hannu wajen murkushe gwamnatin.
Bakin haure 318 da suka fito daga kasashe dabam dabam na yammacin Nahiyar Afrika, kasar Algeria ta taso keyarsu zuwa iyakar ta da Janhuriyar Nijar.
Manyan jami’an Amurka da na Afghanistan da yawa sun tabbatar da wannan matakin, a cewar jaridar.
Bude ofishin jakadancin shine ya kawo karshen ziyarar kwanaki uku da Isaias Afwerki, shugaban Eritrea ya kai Habasha.
Firai Ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu wanda ke ziyarar aiki a kasashen turai yace kasar Iran na iya haddasa kara kwararar 'yan gudun hijira a kasashen Turai idan ba a dauki mataki ba
Tsohon mai bincike na musamman Robert Mueller ya zargi Manafort da yin magana da wasu shaidu akan binciken da ake yi mashi.
Jiragen saman yakin Isra’ila sun kai hare-hare yau Talata a zirin Gaza, inda suka auna wuraren ‘yan kungiyar mayaka masu zafin kishin addinin Islama.
Ana zargin dakarun tsaron Afghanistan na musamman, da dakarun Amurka ke marawa baya da kisan fararen hula guda 9 da kuma raunana wasu su 8 a gabashin lardin Nangarhar, wadanda ga dukan alamu anyi zaton mayakan ISIS ne.
Domin Kari