Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Buratai Ya Zama Jakadan Najeriya A Jamhuriyar Benin


Buratai (hagu) da Minista Onyeama (dama) (Facebook/Ma'aikatar harkokin wajen Najeriya)
Buratai (hagu) da Minista Onyeama (dama) (Facebook/Ma'aikatar harkokin wajen Najeriya)

Kazalika, an nada Janar Abayomi Gabriel Olonisakin mai ritaya wanda shi ne tsohon hafsan hafsoshin Najeriya a matsayin jakadan kasar a Kamaru.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nada Laftanar-Janar Yusuf Buratai mai ritaya, a matsayin jakadan kasar a Jamhuriyar Benin da ke makwabtaka da Najeriyar.

Buratai shi ne tsohon babban hafsan sojin kasa na Najeriya wadanda aka sauke su a watan Janairun bana.

Kazalika, an nada Janar Abayomi Gabriel Olonisakin mai ritaya wanda shi ne tsohon hafsan hafsoshin Najeriya a matsayin jakadan kasar a Kamaru wacce ita ma makwabciya ce ga Najeriyar.

Olonisakin (hagu) Onyeama (dama) (Facebook/Ma'aikatar harkokin wajen Najeriya)
Olonisakin (hagu) Onyeama (dama) (Facebook/Ma'aikatar harkokin wajen Najeriya)

A wani dan kwaryakwaryan biki da aka yi a ma’aikatar harkokin wajen Najeriya a Abuja, Minista Geoffery Enyeama ya mikawa Buratai da Olonisakin wasikun tabbatar masu da mukamansu.

Tun dai a watan Fabrairun da ya gabata, Shugaba Buhari, ya mika sunayen tsoffin manyan hafsoshin sojin kasar hudu ga majalisar dokoki don a tantance su a matsayin jakadu.

Sauran biyun sun hada da Vice Adminiral Ibok-Ete Ibas mai ritaya da Air Marshal Sadique Abubakar mai ritaya

Amma ya zuwa yanzu Buratai da Olonisakin kawai aka nada.

XS
SM
MD
LG