Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kwamitin Sulhu Na MDD Zaiyi Zaman Tattaunawa Kan Birnin Aleppo


Taron Kwamitin sulhu Na MDD
Taron Kwamitin sulhu Na MDD

Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya shirya zaman tattaunawa na gaggawa a yau Laraba sakamakon karuwar tashe tsahen hankula a Birnin Aleppo dake Arewacin Syria.

Birtaniya da Faransa sunyi kiran wannan zama ne wanda Jakadan Rasha a Majalisar dinkin duniya Viatly Churkin ya soka a matsayin “Kamfe na farfaganda”.

Ya biyo bayan tsattsauran hasashen a ranar Talata daga tawagar MDD daga Syria, Staffan De Mistura na yakin da ake a Aleppo yana kara zafi sannan Fararen hula na famar tserewa.

Wata kungiyar Rajin kare hakin dana dam dake Sa ido a Syria, wacce ke da mazauni a Birtaniya, ta bada rahoton kusan mutane dubu 50,000 ne suka tsere Gabashin Aleppo a kwanaki hudu da suka wuce.

Karuwar tashin hankalin ta tilasta wa fararen hula da su gudu su bar gidajen su batare da daukan komai a hannunsu ba, Lamarin da Shugaban Kungiyar Rajin Dan adam ta MDD Stephen O’Brien ya bayyana da “abin lura da kuma tsoratarwa.”

XS
SM
MD
LG