Wani rahoton Hukumar Kula da Duwatsu (USGS) ta Amurka ya bayyana cewar, da safiyar Juma'ar nan, wata girgizar kasa ta afkawa yankin arewa maso gabashin birnin New York mai yawan jama'a, inda mazauna yankin suka bada labarin jin motsin kasa, al'amarin da basu saba ji ba.
Shugaban Amurka Joe Biden ya fada wa Firan ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu a ranar Alhamis cewa ci gaba da samun tallafin Amurka a yakinta da Hamas zai bukaci ta bijiro da matakan kariyar da za su yi amfani da su don kare fararen hula da ma’aikatan jin-kai da ke yunkurin kai musu abinci.
Kalaman na Blinken na zuwa ne biyo bayan ganawar da ya yi da ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar tsaro ta NATO a lokacin da ake dada samun damuwa kan yiwuwar cewa Rasha tana karfafa mataken (makaman) kariyar ta da tallafi daga China, Koriya ta Arewa da Iran.
Da misalin karfe 1 na safe ranar 26 ga Maris ne Larry DeSantis ya nufi aikinsa na biyu a gidan burodin Herman da ke yankin Baltimore.
Rundunar sojin Amurka ta ce a ranar Lahadi dakarunta sun lalata wani jirgi mara matuki a yankin da ke hannun 'yan tawayen Houthi na Yemen da kuma wata hanyar jigilar kaya a tekun Bahar Ahmar.
Masu zanga-zangar sun bukaci gwamnati da ta cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta don kubutar da dimbin mutanen da mayakan Hamas suka yi garkuwa da su a Gaza da kuma gudanar da zabe da wuri.
Tsohon sanatan Amurka kuma wanda jam’iyyar Democrats ta amince ya tsaya takarar mataimakin shugaban kasa karkashinta, Joe Liebeman, ya riga mu gidan gaskiya yana mai shekaru 82 a duniya bayan da ya sha fama da wani rauni sakamakon wata faduwa da ya yi, kamar yadda danginsa su ka fada jiya Laraba.
Jiya Laraba, masu bincike sun fara tattara abubuwan kafa shaida daga cikin jirgin ruwan da ya hankade wani sashin gadar Francis Scott a ranar Talata.
Sama da mako guda bayan da hukumomin jamhuriyar Nijar suka bada sanarwar yanke huldar ayyukan soja da Amurka gwamnatin Amurkar ta ce ta yi na’am da wannan mataki saboda haka nan gaba kadan kasashen biyu zasu tattauna kan hanyoyi mafi amfani wajen kwashe sojojin Amurkan daga kasar.
Ana ci gaba da ƙoƙarin ayyukan ceto akan gadar Baltimore da ta rugurguje, inda masu aikin ceto a karkashin teku suka koma wurin da sanyin safiyar yau Laraba bayan rashin nasara saboda hazo cikin dare
Gwamnan Jihar Maryland, Wes Moore, ya kore yiyuwar harin ta'addanci sakamakon rugujewar wata muhimmiyar gada a birnin Baltimore da safiyar yau talata bayan da wani jirgin ruwan dakon ya afka mata.
Shugaban kasar Amurka, Joe Biden ya ayyana rugujewar gadar Baltimore a matsayin mumunar hatsari inda ya yi alkawarin sake gina babbar tashar jiragen ruwa dake gabashin kasar nan take bayan wata jirgin ruwa ta ci karo da gada
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.