Wani matashi dan shekara 17 ya bude wuta a wata karamar makarantar sakandare ta Iowa a Amurka, a rana ta farkon komawa makaranta bayan hutun hunturu, inda ya kashe wata yarinya ‘yar aji shida tare da raunata wasu biyar a ranar Alhamis yayin da daliban suka yi shinge a ofisoshi a firgice.
A jiya Talata tsohon Shugaban Amurka Donald Trump ya daukaka kara kan hukuncin da sakatariyar harkokin wajen jihar Maine ta jam’iyyar Democrat ta yanke, na haramta masa takara.
"An tabbatar da cewa an kashe Maalim Ayman ne a wani farmakin hadin gwiwa da sojojin kasar Somaliya tare da taimakon sojojin Amurka suka yi a ranar 17 ga watan Disamba," in ji Daud Aweis a shafinsa na X da yammacin ranar Alhamis.
A ranar Litinin da ta gabata ne Hukumar Kula da Hada-Hadar Kudi ta Amurka (SEC) ta gurfanar da dan kasuwan nan na Najeriya Dozy Mmobuosi da wasu kamfanoni uku wanda shi ne shugabansu, inda ake zargin su da damfarar masu zuba jari.
"Kotun koli ta Colorado ta fitar da wani hukunci mai cike da kura-kurai a daren yau kuma za mu shigar da kara cikin gaggawa zuwa kotun kolin Amurka." in ji mai magana da yawun yakin neman zaben Trump
Isira’ila ta kai wasu sabbin hare-hare ta sama a ranar Talata tare da ci gaba da kai hari ta kasa akan mayakan Hamas a Zirin Gaza, yayin da Amurka ta hada kawayenta don kare hanyoyin jiragen ruwa a tekun Bahar Maliya daga ‘yan tawayen Houthi da ke samun goyon bayan Iran a Yemen.
Wasu iyalan Falasdinawa biyu a Amurka sun shigar karar gwamnatin Biden, suna masu cewa gwamnatin ba ta yi wani abu ba wajen kwashe ‘yan uwansu Amurkawa da suka makale a Gaza kamar yadda ta yi wa ‘yan Isra’ila kuma Amurkawa.
'Yan jam'iyyar Republican a Majalisar Wakilan Amurka na ci gaba da kokarin ganin an kada kuri’a a wannan makon, wadda za ta tabbatar da binciken tsige Shugaba Joe Biden. Sai dai babu tabbas kan ko shugabanni na da isassun kuri'u don amincewa da matakin.
Yayin da Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare da ya yi sanadiyar karuwar asarar rayukan fararen hula, Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya yi kira da a yi amfani da wani karfin ikon da ba kasafai ake amfani da shi ba a wannan makon.
Kungiyar vehicle for change na aiki da motocin da aka bayar gudummuwa, su gyara su, sannan da hadin gwuwar hukumomi daban-dabam a daukacin yankin da su ke, sai su gano iyalan da ke bukatar mota domin zuwa wurin aiki ko yin wasu al'amura na rayuwa a basu.
Sabuwar jakadiyar Amurka ta gabatar wa hukumomin rikon kwaryar Nijar takardun kama aiki, kwana daya bayan haka Rasha ta tura karamin ministanta na tsaro zuwa birnin Yamai, ziyarar da masana suka fassara a matsayin wani yunkuri na Rasha na samun matsuguni a Yankin Sahel.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.