A wani bangare na bada gudummuwa wajen ganin Ghana ta shawo kan matsalar abinci, kasar Isra'la ta shirya wani taro tsakanin manoman shinkafa a Ghana da na kasarta a birnin Accra, inda suka tattauna kan matakai da dama.
Sannan za ku ji cewa masu sha’awar tsayawa Republican takarar shugaban kasa na karuwa – za ku ji mutane na baya-baya da ke shirin ayyana burinsu na neman tikitin jam’iyyar.
Yayin da Ghana ta kammala mataki na biyu na bunkasa samar da makamashin nukiliya, gwamnatin Amurka da Japan sun kara jaddada alkawarin tallafa wa shirin makamashin nukiliyar Ghana, da ke da nufin ba da ingantaccen makamashi mai tsabta.
Bayan kimanin watanni ana bincike, an yi nasarar kama wani da ake zargi da harbin da ya kashe Eunice Dwumfour mai shekaru 30 da haihuwa.
Turner ta rasu ranar Talata, bayan doguwar jinya a gidanta dake Küsnacht kusa da Zurich, a cewar manajanta. Ta zama 'yar kasar Switzerland ne shekaru goma da suka wuce.
Yemi Mobolade, dan Najeriya ne kuma dan kasuwa wanda bashi da kwarewa a harkar siyasa, ya zama bakar fata na farko da aka taba zaba a matsayin Magajin Garin Colorado Springs bayan da yayi nasara akan Wayne Williams da daren Talata a zagayen zaben da aka yi a birnin.
Tawagar jami'an da aka kai wa hari ranar Talata a garin Ogbaru na jihar Anambra ta kunshi ‘yan Najeriya guda tara, ciki har da ma’aikatan ofishin jakadancin Amurka a Najeriya biyar da kuma jami’an ‘yan sandan Najeriya hudu.
Amurka ta sha alwashin hana wasu 'yan Najeriya damar shiga kasarta, sakamakon rawar da suka taka wajen yi wa dimokaradiyya zagon kasa a babban zaben kasar na 2023 da aka gudanar.
Sakatariyar Baitul Malin Amurka, Janet Yellen, ta yi gargadin cewa idan har ba a fadada damar karbar bashin ba, nan da farkon watan Yuni gwamnati za ta rasa kudaden da za ta kashe.
Kotu ta umurci Tsohon shugaban Amurka Donald ya biya matar da aka tabbatar ya yi ci zarafinta ta hanyar neman yin lalata da ita shekaru da dama da suka wuce, lamarin da Trump ya sha musantawa a baya.
Zababben shugaban Najeriya, Bola Tinubu, da Dokta Ngozi Okonjo-Iweala, babbar darakta a Cibiyar kasuwanci ta duniya, sun shiga jerin mutane 100 da suka fi tasiri a duniya na shekarar 2023 da Mujallar Time ta fitar.
Ana ci gaba da maida martani game da tuhumar Donald Trump a Amurka inda kawuna suka rabu, wannan dai shi ne karon farko da ake tuhumar wani tsohon shugaba a Amurka.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.