Majalisar Dattawa ta tabbatar da Nusrat Chowdhury, wata lauya mai kare hakkin jama'a, a matsayin Musulma ta farko da ta zama alkalin tarayya a tarihin Amurka.
Tsohon shugaban Amurka Donald Trump, ya isa kulob din Golf dinsa da ke birnin Miami gabanin gurfanar da shi a gaban kuliya bisa zarginsa da laifin karkatar da wasu bayanan sirrin tsaron kasar bayan ya bar fadar White House a shekarar 2021.
Wasu daga cikin 'yan jam'iyyar Rifabulikan da ke hamayya da neman zaben fidda gwanin na Trump sun caccaki zargin samun Trump da laifi.
Tsohon Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ana tuhumarsa da laifin karkatar da wasu takardu na sirri da aka gano a gidansa da ke Florida.
Hayakin da ke fitowa daga gobarar daji a kasar Canada ya kwarara har zuwa Gabashi da Yammacin tsakiyar Amurka a ranar Laraba, ya mamaye manyan biranen kasashen biyu a cikin wani yanayi mai muni.
Wata kungiyar kasar Amurka da ake kira Health and Development International ta sanar cewa jamhuriyar Nijer ta samu nasarori a yunkurin magance matsalar yawan matan da ke mutuwa sanadiyyar zubar da jini a yayin nakuda.
A yau Talata ne aka rantsar da sabon Magajin Garin birnin Colorado Springs na jihar Colorado ta nan Amurka.
Mobolade yayi takara ne a matsayin mai zaman kan sa, ya kuma sami nasarar kayar da wani dan jam'iyyar Republican da ya dade yana rike da mukamin bayan zagaye na biyu na zaben.
A wani bangare na bada gudummuwa wajen ganin Ghana ta shawo kan matsalar abinci, kasar Isra'la ta shirya wani taro tsakanin manoman shinkafa a Ghana da na kasarta a birnin Accra, inda suka tattauna kan matakai da dama.
Sannan za ku ji cewa masu sha’awar tsayawa Republican takarar shugaban kasa na karuwa – za ku ji mutane na baya-baya da ke shirin ayyana burinsu na neman tikitin jam’iyyar.
Yayin da Ghana ta kammala mataki na biyu na bunkasa samar da makamashin nukiliya, gwamnatin Amurka da Japan sun kara jaddada alkawarin tallafa wa shirin makamashin nukiliyar Ghana, da ke da nufin ba da ingantaccen makamashi mai tsabta.
Bayan kimanin watanni ana bincike, an yi nasarar kama wani da ake zargi da harbin da ya kashe Eunice Dwumfour mai shekaru 30 da haihuwa.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.