Hotunan bidiyo sun nuna yadda dubban mutane suke ta bazama akan titunan Dhaka, babban birnin kasar suna nuna farin cikin saukar firaiministar wacce ta kwashe shekaru 15 tana mulkar kasar.
Kungiyar Hezbollah ta kasar Labanon ta ce ta kaddamar da wani harin jirgin sama mara matuki a safiyar yau Litinin a arewacin Isra'ila, inda sojojin Isra'ila suka ce harin ya raunata dakarunta biyu tare da ta da gobara.
Nemour ta samu damar fafatawa a karkashin tutar Algeriya ne bayan da kungiyarta ta samu sabani da hukumar wasannin tasalle-tsallen Faransa ne.
Masu zanga-zanga sun kai hari kan 'yan sanda tare da tada wuta a birnin Sunderland da ke arewa maso gabashin Burtaniyya a ranar Juma'a yayin da tashin hankalin ya bazu zuwa wani garin a arewacin kasar, biyo bayan kisan wasu yara uku a ranar Litinin a Southport.
Wasu ‘yan Najeriyar mazauna wasu kasashe da ke bibiyar al’amuran da ke gudana a kasar da dama sun yarda cewa matsin rayuwar da jama’ar kasar ke fama da ita, wani abin tashin hankali ne da aka jima ba a duba wa ba.
A yau Laraba, Shugaban Turkiyya Recef Tayyib Erdogan, ya yi Allah-wadai da mummunan kisan gillar da aka yiwa amini kuma 'dan uwansa, shugaban kungiyar gwagwamaryar Falasdinawa Musulmai ta Hamas, Isma’il Haniyeh.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Nasser Kanani a sakon ta’aziyya da ya aika kan kashe shugaban Hamas Ismail Haniyeh, ya bayyana cewa za su dauki fansa kan kisan da aka yi wa Haniyeh.
Cibiyar Kula da Cututtuka Masu Yaduwa ta Amurka ta fada a ranar Talata cewa, tana shirin kashe dala miliyan 10 don dakile kamuwa da cutar murar tsuntsaye tsakanin ma’aikatan gona, da ya hada da dala miliyan 5 don rigakafin mura na lokaci-lokaci.
A yau Talata jami’ai suka bayyana cewa, zaftarewar kasar da aka samu a wurare da dama a kudancin Indiya ta hallaka mutane 93 sannan ana fargabar kasa ta birne wasu mutanen da dama.
Binciken da rundunar ‘yan sandan kasa da kasa (INTERPOL) ta gudanar ya nuna cewa duk bayan sa’a guda, ana fitar da dubban daruruwan dalolin haramun daga Najeriya zuwa sauran sassan duniya.
Isra'ila ta ce tana son ta dauki fansa kan harin da Hezbollah ta kai mata, sai dai ta ce ba ta son ta jefa Gabas ta Tsakiya cikin yaki tsundum, kamar yadda wasu jami'an Isra'ila biyu suka fada a ranar Litinin.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.