Farin da ya faro tun a farkon shekarar nan ta 2024, kuma ya shafi amfanin gona da kiwo, lamarin da ya janyo karancin abinci da kuma illa ga tattalin arzikin kasashe da dama.
Hukumar zaben kasar da 'yan adawa ke kallonta a matsayin wani bangare na jam'iyya mai mulki, ta ce shugaba Nicolas Maduro ne ya yi nasarar samun wa'adin mulki na uku, a zaben da aka gudanar a ranar 28 ga watan Yuli, da kasa da kashi 52% na kuri'un da aka kada.
Hukumar tsaron fararen hula a Gaza ta fada cewa, wani harin da Isira’ila ta kai da sanyin safiyar ranar Asabar ya kashe mutane 15 daga wani iyalan Falasdinawa, da su ka hada da yara tara da mata uku.
Rikicin na yanzu ya sanya Dubai ta sake amfani da damar domin samun riba, kamar yadda ta yi a lokacin annobar COVID-19 da kuma mamayar Rasha a Ukraine.
Wani jami’in karamar hukumar ya ce rikicin ya biyo ne bayan wata zanga-zangar nuna fushin fursunonin kan yanayin zaman gidan yarin, da a cewarsa, ya hada da karancin abinci da rashin lafiya.
Ofishin jakadancin China da ke Tokyo ne ya ba da wannan gargadin bayan wata ziyara da wasu gungun ‘yan majalisar dokokin Japan suka kai a kasar Taiwan a wannan makon, ciki har da tsohon ministan tsaro Shigeru Ishiba, dan takarar da ake hasashen zai iya zama Prime ministan kasar na gaba.
Shugabannin kasashen Faransa, Jamus da Birtaniya sun amince da kiran tsagaita wuta a Gaza, da mayar da dumbin mutanen da Hamas ta yi garkuwa da su da kuma kai agajin kayayyakin jin-kai ba tare da wata tangarda ba.
Wannan shi ne na baya-bayan nan na abin da ofishin kare hakkin bil Adama na Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana da "Hare-hare kan makarantu a wayance" na Isra'ila, tare da a kalla hare-hare 21, tun daga ranar 4 ga watan Yuli, inda kuma suka hallaka daruruwan mutane, ciki har da mata da kananan yara.
Yunus mai shekaru 84, da ya taba lashe lashe kyautar Nobel, ya dawo daga Turai a wannan makon don jagorantar gwamnatin wucin gadi, da ke fuskantar babban kalubale na kawo karshen rikice-rikice da aiwatar da sauye-sauyen demokradiyya.
Dakarun Ukraine sun kai farmaki a yankunan kan iyakar da safiyar Talata, a wani hari da ya kasance mafi girma da samun nasara da Kyiv kai a cikin shekaru 2 da rabi na yakin.
Hukumar kare fararen hula ta Gaza ta fada a yau Asabar cewa, adadin wadanda suka mutu sakamakon harin sama na baya bayan nan da Isira’ila ta kai kan wata makaranta da Falasdinawa ke zaune wadanda suka rasa matsugununsu ya haura 90.
Tallafin zai kumshi makamai da karin kayan aiki, wanda zai kasance kunshin tallafi na 10 da Amurka ta aika zuwa Ukraine, tun lokacin da shugaba Joe Biden ya rattaba hannu kan dokar tallafawa tsaron Ukraine a watan Afrilu.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.