Rundunar sojin Najeriya ta ce zata ci gaba da horar da jami’anta don tinkarar kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta da zummar magance su.
Mata daga wasu yankunan da aka samu rikice-rikice a sassan jahar Filato, sun gano cewa kafa kungiyoyin fadakarwa kan zaman lafiya sun fara yin tasiri, ganin yadda aka samu kwanciyar hankali a yanzu.
Jami’iyyun siyasa a jahar Filato sun kuduri aniyar daura damara don shiga manyan zabubbukan da ke gabatowa a shekarar badi.
Ranar bakwai ga watan Fabrairun kowace shekara ne gwamnatin jihar Filato ta ayyana a matsayin ranar yafiya bisa rikice-rikicen da jihar ta fuskanta a baya.
A ci gaba da bikin ranar Hijabi ta duniya, mata da ‘yan mata a jahar Filato sun jaddada muhimmancin sanya Hijabi ga mace, don kare mutuncinta, da na addininta, da rage cin zarafin mata da ke yawaita.
Gwamnatin jihar Filato ta ce ta bullo da wani sabon tsari na fadakar da al’umma kan su sanya ido kan makwabtansu, don gano wadanda ke fakewa suna kashe mutane da yin garkuwa da su.
Wasu hare-hare a kauyen Dong dake kan iyakar kananan hukumomin Jos ta Arewa da Bassa, sun yi sanadin rasa rayukan mutum biyar a yammacin ranar Asabar.
Dakarun dake aikin wanzar da zaman lafiya a jahar Filato sunyi nasarar hallaka wasu masu garkuwa da mutane su uku, suka kuma kwace makamai.
Hukumar ta NCDC ta ce mutum dari da biyu ne suka mutu da cutar ta Lassa a Najeriya a bara.
Jihar Filato ta sha fama da matsalolin hare-haren da kan kai ga asarara rayuka da dumbin dukiyoyi.
Wani sabon rikici tsakanin al’ummomin Tibi da Fulani a kananan hukumomin Lafiya da Obi a jihar Nasarawa, ya yi sanadin rasa rayuka da dama.
Majinyata a asibitin kwararru a jahar Filato sun shiga hali mara dadi, bayan daukacin ma’aikatan dake asibitin, in banda likitoci, suka shiga yajin aiki na sai yadda hali yayi.
Hukumar gidan gyara hali dake jahar Filato ta tabbatar da hari da ‘yan bindiga suka kai wa gidan yari.
Kungiyoyin kwadago na cibiyoyin bincike a Najeriya sun bukaci shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya ceto cibiyoyin daga durkushewa, saboda halin tagayyara da cibiyoyin ke ciki.
Rahotanni sun ce tun da safiyar ranar Alhamis aka tsaurara matakan tsaro a kewayen majalisar, wani abu da ya yi nuni da cewa akwai abin da ke faruwa.
Kungiyar Fuiani makiyaya ta Miyetti Allah Cattle Breeders, shiyyar Arewa ta tsakiyar Najeriya ta gudanar da gagarumin taro a garin Lafiya, jihar Nasarawa don jan hankalin Fulani su yaki jahilci ta hanyar sanya ‘ya’yansu a makarantun addini da na zamani.
Babban hafsan sojin Najeriya, Laftanar Janar Faruk Yahaya ya ce sojin Najeriyar za su ci gaba da aiki tare da gwamnatin Jihar Filato don maido da zaman lafiya da tsaro a cikin jihar.
Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta gurfanar da mutum goma a gaban babban kotun jihar Filato wadanda take zargi da hannu a kisan wasu matafiya a Rukuba Road kan hanyarsu zuwa jihar Ondo.
Kungiyar al’ummomin dake jihohin tsakiyar Najeriya wato Middle Belt Forum ta kalubalanci gwamnatin tarayya da ta bayyana sunayan wadanda ke tallafawa kungiyar Boko Haram.
Domin Kari