Wasu rumfunan zabe a babban birnin tarayyar Najeriya sun kasance da dogayen layuka har cikin daren Asabar yayin da masu kada kuri'a su ke jira don su kada kuru'unsu.
Masu zabe a sassa daban-daban na Abuja sun nuna gamsuwa kan aikin na’urar tanatnce masu kada kuri’a wato BVAS da hukumar zabe ke amfani da ita a babban zaben da bugin kirjin hanya ce ta magance magudin zabe.
Hukumar zaben Najeriya ta INEC ta ce bayanai na nuna cewa akwai kwanciyar hankalin gudanar da babban zaben a kasar yau Asabar.
Hukumar kula da kafafen labarai na ketare ta Amurka wato USAGM, ta hori wakilan kafafen labaru na Najeriya kan yadda za su tsare dokokin aikin jarida idan sun tashi ba da labarai kan yadda za a gudanar da babban zabe har zuwa bayan sanar da sakamako.
Shirin na wannan makon na tattaunawa ne akan bukatar kafa cibiyoyin kudi a Arewa da sauran hanyoyin raya arziki musamman a yankunan karkara.
A cikin shirin na wannan makon, mun duba batun kawo shawara ce ta kafa bankuna mallakar yankin Arewa da rassa a dukkan Jihohin Arewa 19 don matso da bankuna kusa da jama’a musamman mazauna karkara.
Kwana daya gabanin gudanar da gangamin yakin neman zabe na jam’iyyar PDP a jihar Ribas, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Atiku Abubakar ya janye kamfen din don abin da a ka zaiyana da gudun asarar rayuka.
A cikin shirin na wannan makon, mun duba batun bunkasa harkokin ilimi a yankin Arewacin Najeriya, inda yara kanana da dama ba sa zuwa makaranta ko kuma su na gararamba kan tituna ba tare da samun kulawar da ta dace daga gwamnatoci da kuma iyaye ba.
Tawagar masu ziyara daga Najeriya zuwa birnin Kaulaha a Senegal da su ka tsallake rijiya da baya a kisan gillar da jami’an tsaro su ka yi musu a Burkina Faso sun isa Kaulaha.
Kungiyar Ansarul Din Attijjaniyya da ke zama uwar kungiyoyin darikar Tijjaniyya ta yi Allah wadai ba bude wuta kan wata tawagar 'ya'yanta daga Najeriya da sojoji suka yi a Burkina Faso a kan hanyarsu ta zuwa birnin Kaulaha na kasar Senegal.
A cikin shirin na wannan makon, mun duba muhimmancin kafa tasoshn sauke hajar teku a tudu a yankin Arewacin Najeriya da ba ya kusa da gabar teku.
Karin kwana goma da babban bankin Najeriya ya yi don canja tsoffin kudi ya rage zullumin jama'a da ke fafutukar yin canjin.
Dan takarar Shugaban kasa na NNPP, Rabi'u Kwankwaso, ya ce ba wanda zai yi asarar kudin sa matukar ya hau karagar mulki.
A cikin shirin na wannan makon, bangare ne na karshe da ya duba yadda tarihin yankin Arewa ya ke a baya inda mutane kan taimakawa juna ta hanyar marabtar baki, kyautata makwabta, tallafawa marayu da sauran su.
Masana na baiyana cewa sai ‘yan Najeriya a dukkan sassa sun yi zabe nagari ba da la’akari da wani bambanci ba ne za a iya samun cin gajiyar arzikin kasar mai yawa.
Domin Kari