A lokacin gaisuwar idin karamar sallah da al’ummar Abuja da a ka canka karkashin ministan Abuja Muhammad Musa Bello zuwa fadar Aso Rock, shugaban ya nemi ahuwar jama’a a kusan shekaru 8 da ya yi ya na mulkin kasar.
Hukumar zaben Najeriya INEC ta mika batun binciken kwamishinan ta na zabe a jihar Adamawa Barista Ari Hudu ga babban sufeton ‘yan sanda Baba Usman Alkali don daukar matakin doka da ya dace.
An shiga rufe tafsirin azumin watan ramadan na shekarar bana ta hijira 1444 a manyan majalisun tafsirin a sassan Najeriya daban-daban don shirin idin karamar sallah ko tafiya Saudiyya don umrah.
Hukumar zaben Najeriya INEC ta dakatar da shugaban hukumar na jihar Adamawa daga shiga ofishin ko kusantar ofishin har sai an dauki mataki na gaba.
Hukumar zaben Najeriya INEC ta ce kwamishinan zabenta a Adamawa ya yi gaggawar fadin sakamakon zabe ba tare da kammala tattara sakamakon ba.
Jihar Adamawa a arewa maso gabar da Kebbi a arewa maso yammacin Najeriya na cikin shirin kammala zaben gwamnoninsu Asabar din nan.
Kafafen labarun Najeriya sun fara yayata sunayen wasu manyan 'yan jam'iyyar APC da a ke tallatawa don samun mukamai a gwamnatin Tinubu.
Tun da farko, wadanda suka samu umurnin kotu na dakatar da Abure sun yi dafifi a helkwatar jam’iyyar don hana shi yin jagaoranci.
Malaman Islama da addinin Kiristan nan biyu wato Imam Nuraini Ashafa da Pastor James Wuye sun nuna cewa hadin kan jama’a ta hanyar kauce wa bambance-bambance ne zai dawo da Najeriya kan turba mai kyau ta zaman lafiya.
Ofishin kamfen din dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Leba ya nuna damuwa ainun kan zargin cin amanar kasa da gwamnatin Najeriya ta yi wa Peter Obi.
Kananan ‘yan kasuwa da ke hada-hadar su a unguwar Mpape da ke gefen Abuja, inda talakawa su ka fi zama, sun kaure da murnar dakatar da mamaye musu kasuwa da kotu ta yi.
Mataimakin shugaban babbar jam’iyyar adawar Najeriya PDP Umar Iliya Damagun ya zama mukaddashin shugaban jam’iyyar bayan saukar wucin gadi da shugaban ta Iyorchia Ayu ya yi sakamakon umurnin babbar kotun jihar Binuwai.
Kwamitin majalisar wakilan Najeriya ya yi zama inda ya karbi shawarwarin jama’a kan kudurin kafa hukumar kula da almajirai da ke ragaita kan tituna musamman na arewacin Najeriya.
Kungiyar kwadagon Najeriya NLC za ta fara gagarumin yajin aiki daga ranar laraba mai zuwa don nuna fusata da yanda gwamnati ta kasa wadatar da ma'aikata da takardun kudin da za su rika yin cefane.
Jinkirin sanar da sakamakon zabe a jihar Zamfara ya jawo muhawara tsakanin dan takarar babbar jam’iyyar adawa PDP, Dauda Lawal da kuma bangaren gwamnan jihar Bello Matawalle na APC.
Masu kada kuri’a basu fita zabe yadda ya kamata ba a karamar hukumar Karu wadda ta fi yawan jama’a a jihar Nasarawa da ke makwabtaka da Abuja babban birnin tarayyar Najeriya.
Domin Kari