Blinken ya kore duk sukar da ake yi wa hukumomin Washington cewa ba su kimtsa da kyau ba, duba da yadda rundunar dakarun Afghanistan ta durkushe cikin sauri.
Sai dai Abdullah Abdullah, wanda shi ke jagorantar majalisar sasantawa a kasar, ya wallafa wani sakon bidiyo a Facebook, yana sukar Ghani.
“Daukan matakin ya zama dole saboda rahotannin da aka tattara kan tsaro sun nuna cewa akwai barazana ga rayuka da dukiyoyin jama’a.”
“Tun daga lokacin da aka kafa Najeriya har zuwa rasuwarsa, Joda ya ba da gagarumar gudunmowa wajen hadin kai da ci gaban kasar.”
Ofishin zai ci gaba da kasancewa a rufe har tsawon kwana goma kamar yadda dokar yaki da cutar ta coronavirus ta tanada a Burtaniya.
Dan wasan da ya fi haskawa a wasan shi ne, mai tsaron ragar Chelsea Kepa Arrizabalaga saboda kade fenariti biyu da ya yi.
A cewar gwamna Zulum, ba an gudanar da jarabawar ba ne don a kori wani malami a aiki, sai dai don a auna kwarewarsu don a san inda za a saka su.
A makon da ya gabata gwamna Masari ya yi kira ga dakarun kasar da su tsaurara matakan tsaro a jihar, inda ya ce a kullum sai ‘yan bindiga sun kai hari a kananan hukumomi 10 cikin 34 da ke jihar.
“‘Yan tsirarun mutanen da ke son ya yi murabus su fito karara su fadawa mambobin jam’iyyar da ke duka fadin kasar, laifin da ya yi da suke so ya yi murabus.”
Gwamnatin jihar Kaduna da ke arewa maso yammacin Najeriya, ta ce an kashe wasu kangarurrun ‘yan fashin daji hudu da suka addabi yankunan jihar.
A ranar 28 ga watan Yuli, Ruth da wani mutum da ta aura, suka mika kansu ga dakarun Najeriya a wani yanki da ke Bama, a cewar wata sanarwa da kakakin gwamna Zulum Malam Isa Gusau ya fitar a karshen mako.
Babbar jam’iyyar adawa ta PDP a Najeriya ta ce miliyoyin ‘yan Najeriya sun zaku su yi rijista da jam’iyyar yayin da take shirin fara aikin sabunta rijista ta yanar gizo a duk fadin kasar.
Mutanen kuma da ke fama da cutar a yanzu haka sun kai 9, 542 yayin da jimullar mutanen da cutar ta harba ya kai 177, 142 a cewar NCDC.
Baya ga mutum daya da ya mutu wasu mutum biyar sun jikkata wadanda aka kai su asibiti don samun kulawa.
Rundunar sojin Najeriya ta ce ana samun karin mayakan Boko Haram da na ISWAP da ke ajiye makamansu su mika wuya.
“FC Barcelona na mika godiyarta ga dan wasan bisa irin rawar da ya taka wajen dabbaka kungiyar, tana kuma masa fatan alheri a duk in da zai je.”
“Shi da kansa Kyari ya wallafa bidiyon a shafinsa na Facebook a ranar 30 ga watan Yuni, jim kadan bayan ziyarar.”
An dai yi bikin karramawar ne a Zinder wanda yana daga cikin jerin shagulgulan da aka yi don murnar wannan rana ta samun ‘yancin kai.
A ‘yan kwanakin nan an yi ta rade-radin cewa Tinubu na fama da rashin lafiya a London.
Hukumomi a jihar sun ce ba a hada allurar riga-kafin Moderna da ta Astrazeneca suna masu cewa dole ne mutum ya tsaya akan guda daya.
Domin Kari