Taliban ta mulki Afghanistan daga 1996 zuwa 2001 inda ta gudanar da mulkinta karkashin shari’ar Musulunci a kasar. Ga wasu daga cikin muhimman abubuwa da suka shafi akida da tarihin kungiyar.
"Gwamnatin Ganduje ta mai da hankali ne kan kammalawa da aiwatar da manyan manufofi da shirye -shirye tare da muhimman ayyukan samar da ababen more rayuwa tsakanin yanzu zuwa 2023."
A ranar Litinin, rahotanni daga Sifaniya sun bayyana cewa dan wasan wanda dan asalin kasar Portugal ne, na shirin komawa Real Madrid da ya baro a 2018.
Mawaki kuma jarumin Kannywood Garzali Mika’ilu, wanda aka fi sani da Garzali Miko ko Gaza, na shirin shiga daga ciki.
A cewar Farfesa Danbatta, sarrafa ilimin ta yin shi a aikace ta hanyar da ta dace, zai taimakawa matasa wajen samun ayyukan da za su rage dogaron da suke yi da ayyukan gwamnati.
A lokacin wasan, an soke kwallayen Haaland da Youssoufa Moukoko bayan da alkalin wasa ya ayyana cewa sun yi satar gida.
“Ci gaba da zaman dakarun Amurka a kasar na tsawon shekara daya ko shekara biyar ba zai sauya komai ba idan har sojojin Afghanistan ba za su iya rike kasarsu ba,” Biden ya fada a ranar Asabar cikin wata sanarawa.
Shugaban Najeriya Muhammdu Buhari da tawagar da ta raka shi London sun kebe kansa bayan da suka dawo a ranar Juma'a, a wani mataki na bin ka’idar da aka shimfida ga wadanda suka je kasashen ketare don a kaucewa yiwuwar yada cutar COVID-19.
Blinken ya kore duk sukar da ake yi wa hukumomin Washington cewa ba su kimtsa da kyau ba, duba da yadda rundunar dakarun Afghanistan ta durkushe cikin sauri.
Sai dai Abdullah Abdullah, wanda shi ke jagorantar majalisar sasantawa a kasar, ya wallafa wani sakon bidiyo a Facebook, yana sukar Ghani.
“Daukan matakin ya zama dole saboda rahotannin da aka tattara kan tsaro sun nuna cewa akwai barazana ga rayuka da dukiyoyin jama’a.”
“Tun daga lokacin da aka kafa Najeriya har zuwa rasuwarsa, Joda ya ba da gagarumar gudunmowa wajen hadin kai da ci gaban kasar.”
Ofishin zai ci gaba da kasancewa a rufe har tsawon kwana goma kamar yadda dokar yaki da cutar ta coronavirus ta tanada a Burtaniya.
Dan wasan da ya fi haskawa a wasan shi ne, mai tsaron ragar Chelsea Kepa Arrizabalaga saboda kade fenariti biyu da ya yi.
A cewar gwamna Zulum, ba an gudanar da jarabawar ba ne don a kori wani malami a aiki, sai dai don a auna kwarewarsu don a san inda za a saka su.
A makon da ya gabata gwamna Masari ya yi kira ga dakarun kasar da su tsaurara matakan tsaro a jihar, inda ya ce a kullum sai ‘yan bindiga sun kai hari a kananan hukumomi 10 cikin 34 da ke jihar.
“‘Yan tsirarun mutanen da ke son ya yi murabus su fito karara su fadawa mambobin jam’iyyar da ke duka fadin kasar, laifin da ya yi da suke so ya yi murabus.”
Gwamnatin jihar Kaduna da ke arewa maso yammacin Najeriya, ta ce an kashe wasu kangarurrun ‘yan fashin daji hudu da suka addabi yankunan jihar.
A ranar 28 ga watan Yuli, Ruth da wani mutum da ta aura, suka mika kansu ga dakarun Najeriya a wani yanki da ke Bama, a cewar wata sanarwa da kakakin gwamna Zulum Malam Isa Gusau ya fitar a karshen mako.
Domin Kari