Marigayin ya rike mukamin mataimakin gwamnan babban bankin na Najeriya a tsakanin 2005 zuwa 2007. Sannan ya taba aiki a bankin raya kasashen Afirka na AFDB.
Manchester United, wacce za ta kara da West Ham United a ranar Lahadi ta koma matsayi na biyu a teburin gasar.
A ranar Juma'a Fani-Kayode, wanda ya yi fice wajen sukar lamirin gwamnatin Buhari, ya koma jam'iyyar APC mai mulki yayin da shi kuma Matawalle tun a watan Yuli ya koma jam'iyyar.
A ranar 24 ga watan Agusta ‘yan fashin daji suka kutsa kai cikin kwalejin ta NDA suka kashe sojoji biyu tare da yin garkuwa da Datong.
Infantino na ziyarar kwana shida ne a Najeriya inda yake halartar gasar kwallon kafa ta mata da uwargidan shugaban kasa Aisha Buhari ta shirya a tsakanin kasashe shida wacce ke gudana a Legas.
Fani-Kayode ya kasance daya daga cikin masu sukar lamirin gwamnatin APC mai mulki kan yadda take tafiyar da sha'anin mulkinta.
Rahotanni sun ce shugaban na EFCC ya yanke jiki ya fadi a fadar shugaban kasa da ke Abuja, yayin da yake gabatar da jawabi a wani taro.
A kwanakin baya kotu ta ba da umarnin a gudanar da gwajin lafiyar kwakwalwar Sheikh Abduljabbar, wanda sakamakon bincike ya nuna cewa lafiyarsa kalau kamar yadda rahotanni suka nuna.
Bayanai sun yi nuni da cewa, Bawa na cikin magana sai aka ji ya shiru, jim kadan bayan hakan sai aka ka ga ya kare fuskarsa da hannunsa yana mai cewa a yi hakuri ba zai iya ci gaba da magana ba.
A farkon 2017, wani jirgin sojojin Najeriya ya taba kai hari bisa kuskure akan wani sansanin ‘yan gudun hijira da ke Rann a jihar Borno, inda mutane kusan 100 suka rasa rayukansu.
Liverpool ta lallasa AC Milan da ci 3-2 a wasansu na farko da suka buga a gasar cin kofin zakarun nahiyar turai na Champions League a wannan sabuwar kakar wasa
Ita dai kungiyar ta IPOB ta sha musanta hannu a kisan jami’an tsaron Najeriya da hare-hare da ake kai wa a kudu maso gabashin kasar.
Sai dai masu sharhi a fagen kwallon kafa na ganin, ita ma West Ham ba kanwar lasa ba ce, suna masu cewa, komai na iya faruwa a wasan.
Dan wasan Young Boys Siebatcheu ne ya ceto kungiyarsa gab da ana shirin kammala wasan bayan karin lokaci da aka yi.
Bayanai sun yi nuni da cewa ‘yan bindigar sun sace basaraken ne da yammacin ranar Talata akan hanyar Abuja zuwa Kaduna.
Rahotanni sun ce 'yan Najeriya shida da ake nema, sunayensu sun fito ne cikin jerin mutum 38 daga kasashe daban-daban da kasar ta ayyana cewa tana farautarsu ruwa a jallo.
“Ina sane da cewa akwai matsalolin da ke shafar ayyukan da muke yi a sassan kasar nan, amma ina muku albishir da cewa, ana kan daukan matakan da za su kawo karshen wadannan kalubale.”
Ole Gunnar Solskjaer ya kuma yi fatan idan Manchester United ta lashe kofuna, hakan zai ba Paul Pogba kwarin gwiwar ci gaba da zama a kulob din.
Tankar man ta fadi ne yayin da direbanta ke kokain shiga shataletalen da ake kira Maidoki a birnin Yola da ke jihar Adamawa a arewa maso gabashin Najeriya.
Domin Kari