Ganin yadda 'yan-bindiga ke neman sauya salo ta hanyar kai hare-hare wuraren ibada ya sa rundunar 'Yan-sandan jahar Kaduna kafa wani Kwamitin binciko musabbabin sabon salon harin don dakile shi.
Rundunar 'yan sandan jihar Kaduna ta tabbatar da harin da wasu mahara dauke makamai a kan babura suka kai a gundumar Saya-Saya da ke karamar hukumar Ikara ta Jihar Kaduna, inda su ka kashe mutane a cikin masallaci a daren Juma'a.
Duk da sanar da samar da tallafin kudi da kayan abunci da gwamnatin tarayya ta yi don rage radadin kuncin rayuwa a Najeriya, Majalisar Malaman addinin Musulunci ta kasa ta ce tallafin ba zai yi wani tasiri ba.
Bayan karewar wa'adin da kungiyar ECOWAS ta baiwa Sojojin da su ka yi Juyin Mulkin Nijar, yanzu hankali ya koma kan taron da shugaban kungiyar ECOWAS, Shugaba Tinubu ya kira a ranar Alhamis.
Kwararru da masana na ci gaba da zakulo abubuwan da su ke ganin ka iya zama dalilan da, zuwa yanzu, suka hana amincewa da sunan tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasuru Ahmed El-rufa'i a matsayin Ministan Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Al'ummar yankin Birnin Gwari sun ce akwai yuyiwar samun barazanar yunwa saboda manoma da dama sun kauracewa gonakin su sakamakon hare-haren 'yan-bindiga a yankin.
Duk da kai-komon da aka sha yi don baiwa sarakuna gurbi a kundin tsarin mulkin Najeriya ba tare da nasara ba, sabon shugaban majalissar wakilai a Najeriya, Hon. Abbas Tajuddeen ya ce za su dawo da kudin saka sarakuna cikin sha'anin mulki a kundin tsarin Mulkin Najeriya.
Mai martaba Sarkin Zazzau Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli wanda kuma shi ya jagoran Alhazan jihar Kaduna a matsayin Amirul Hajjin bana, ya ce aikin hajjin bana na cike da matsaloli da ya kamata mahukunta su duba domin su sauya salo.
Tun bayan bayyana bukatar sulha da 'yan-bindiga da tsohon gwamnan jahar Zamfara, Sanata Sani Ahmed Yariman Bakura ya yi lokacin da ya ziyarci Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, wasu manyan kasa da masana tsaro su ka fara tattauna batun don nemo mafita.
Domin Kari