Yadda a karon farko a tarihin Amurka, an tsige kakakin majalisar wakilan kasar, Kevin McCarthy na jam’iyyar Republican, wanda shi ne ke mataki na biyu na wadanda za su iya maye gurbin shugaban kasa idan aka samu gibi.
A wata hira da Muryar Amurka Kwamared Audu Titus Amba, mataimakin shugaban kungiyar kwadago ta NLC ya ce karin albashi zai shafi sauran ma’aikatan gwamnatocin jihohi da kananan hukumomi da ma bangarori masu zaman kansu.
Wasu dalilan da suka sa a farkon makon nan kungiyoyin ‘yan kwadago a Najeriya suka janye shirinsu na shiga yajin aikin gama-gari wanda suka so farawa daga ranar 3 ga watan Oktoba
Wani dattijo mazaunin Abuja mai suna Tanko Yakasai, wanda ya tasam ma shekaru 100 a duniya. Ya yi mana bayani game da yadda yake kula da lafiyar shi.
Kwararu sun ce asa’ilin da shekarun mutane suke ja, ya yiwu su fuskanci matsalolin lafiyar da suka zama ruwan dare tsakanin dattawa kamar yanar ido, rashin ji, cutar sukari, ciwon baya da na wuya.
A al’ummar kasashen Afirka, tsofaffi suna da daraja da mahimmanci wajen raya al’adun gargajiya kana suna kasancewa tamkar madubin duba ga matasa. Ko da yake, tsufa na zuwa da irin nasa kalubaloli daban-daban da suka hada da matsalolin lafiya da kuma wadatattacen kulawar lafiya.
Majalisar dokokin Ghana ta kada kuri’ar da za ta bada dama a hukunta duk wanda ya zargi tsofaffi da maita. Idan a ka yi nasarar tabbatar da sabuwar dokar, za ta bada dama a rufe sansanonin sama da mutane 500 da ake zargi da maita.
A wata hira da Muryar Amurka, Sanata Ireti Kingibe, ‘yar Majalisar Dattijan Najeriya ta ce saboda irin kalubalen da ita ta fuskanta a siyasa babban abin da ta fi mayar da hankali akai yanzu, shine samar da dama ga mata da yawa na yin nasara a siyasa
Kungiyoyin kwadago a Najeriya suna barazanar tafiya yajin aiki, inda suka bukaci gwamnati da ta dawo da biyan kudin tallafin man fetur da ta kawo karshe a watan Mayu.
A kasar Guinea, majinyata da dama suna rungumar hanyar kiwon lafiya na gargajiya domin kula da lafiyar su, kazalika, akwai masu irin wannan sana’ar da dama a babban birnin kasar na Conakry.
Yayin da kamfanoni da sauran masu sana’o’i ke ci gaba da tafka asara sakamakon karancin wutar lantarki a Nijar, wasu kugiyoyin fararen hula a kasar sun yi barazanar maka Najeriya a gaban kotun ECOWAS kan zargin saba yarjejeniyar kasuwancin wutar lantarki tsakanin kasashen biyu,
Yayin da kamfanoni da sauran masu sana’o’i ke ci gaba da tafka asara sakamakon karancin wutar lantarki a Nijar, wasu kugiyoyin fararen hula a kasar sun yi barazanar maka Najeriya a gaban kotun ECOWAS kan zargin saba yarjejeniyar kasuwancin wutar lantarki tsakanin kasashen biyu, da wasu rahotanni
Mun tattauna da Malam Kabir Adamu wani mai sharhi kan sha’anin tsaro, akan matsalar yawan sace dalibai a Najeriya, da wasu ke ganin akwai sakacin hukuma sosai.
Matsalar yawan sace dalibai a Najeriya da ‘yan bindiga ke yi a makarantu - A ranar Juma’a 22 ga watan Satumba wasu ‘yan bindiga sun kai hari a wasu dakunan kwanan daliban jami’ar gwamnatin tarayya dake Gusau a jihar Zamfara, inda suka sace kimanin dalibai 24 akasarinsu mata
Zainab Ujudud Shariff kwararriya kan magungunan gargajiya a Najeriya kuma tsohuwar daraktar Sashin Bunkasa Maganin Gargajiya a Ma’aikatar Lafiya ta Najeriya, ta yi mana karin bayani a game da alfanun magungunan.
Maganin gargajiya ya kunshi abubuwa da dama na gargajiya da na zamani wanda ya samo tushe daga al’adun gargajiya da ake amfani da su tun iyaye da kakanni wajen kariya, ganowa da kuma magance jerin cututtuka na bayyane da kuma cututtukan tabin hankali, a cewar kungiyar hukumar ta Duniya WHO.
Wadannan bala’o’I suna faruwa ne lokaci guda sannan suna kai wa ga yiwa mutane rauni, haifar da barazanar lafiyar al’umma sannan su haifar da mumunar barna da asara dake haifar da matsala wajen samar da kulawa ga wadanda suke da bukata.
Abdulshahid Sarki, Kwararren likita a asibitin kasa dake Abuja, ya yi mana bayani a game da matakan da suka kamata mutane su dauka don tunkarar al’amari na daukin gaggawa.
Ra’ayoyin wasu mutane daga Najeriya game da irin matakan gaggawa da suke dauka na taimakon kan su idan bukata ta taso.
Shugabannin kasashen duniya sun sanar da takwarorinsu matsaloli da kuma manufofinsu; Dalilai da ya sa manufofin da ake cimmawa a wajen irin wannan taro ba sa kai labari; Manufar da hukuncin kotun kararrakin zabe a jihar Kano ke nunawa, da wasu rahotanni
Domin Kari