Hukumar Kwallon kafa ta Amurka ta yi Allah wadai da kalaman nuna wariyar launin fata ga ‘yan wasanta a ranar Alhamis, bayan da Panama ta yi nasara a kan Amurka da ci 2-1 a gasar cikin kofin Copa America.
Amurkawa sun bayyana batutuwa da su ke da muhimmanci a zaben shugaban kasa da za a gudanar a watan Nuwamba da suke neman amsa a muhawarar da 'yan takarar Shugaban kasa suka fafata karon farko a kakar zaben bana.
Shugaban Amurka Joe Biden da tsohon shugaban kasar Donald Trump sun gwabza muhawara a daren Alhamis, inda suka fafata kan tattalin arzikin Amurka da harkokin kasashen waje da hakkin zubar da ciki da kuma batun kaura daga kan iyakar Mexico zuwa Amurka.
Kungiyar masu aiko da rahotanni ta Fadar White House ta fada a ranar Alhamis cewa gidan talabijin na CNN ya yi watsi da bukatar baiwa wakilanta damar shiga zauren muhawarar farko ta shugaban kasa tsakanin shugaba mai ci Joe Biden da abokin hamayyarsa Donald Trump na jam’iyyar Republican.
Donald Trump da Joe Biden zasu yi muhawararsu ta farko akan yakin neman zabensu, inda kowannensu ke fada wa masu kada kuri'a cewa, zaben dayan zai zama babban kuskure
Wadansu ma’aurata daga Bowie, jihar Maryland na daga cikin sama da mutane dubu daya da suka rasu sakamakon matsanancin zafi yayin aikin hajjin bana a kasar Saudiya.
Miliyoyin Amurkawa sun sake fuskantar yanayin zafi mai tsanani a jiya Lahadi a fadin kasar, yayin da mummunar ambaliyar ruwa ta mamaye sassan yamma maso tsakiyar Amurka, ciki har da wani gari a jihar Iowa wanda shima ya cika da ruwa.
Jarumi Kiefer Sutherland ya wallafa a shafinsa na X cewa, “Cikin alhini ina sanar da ku mutuwar mahaifina, Donald Sutherland.”
Shugaba Joe Biden ya sanar da wani sabon tsari da zai ba wadanda su ka auri Amurkawa, da kuma 'ya'yan mutanen da su ka auri Amurkawa, izinin zama kasar din-din-din.
A yau Talata ake sa ran Shugaban Amurka Joe Biden zai sanar da wani gagarumin sabon shirin da zai kawar da barazanar mayar da dubban mutanen da suka auri yan kasar Amurka zuwa gida.
An tuhumi wani dan jihar Arizona bisa laifuka hudu da suka shafi safarar bindigogi bayan da masu gabatar da kara na gwamnatin tarayya suka ce wani samame da aka gudanar a boye ya nuna cewa ya shirya kashe bakaken fata a wani harin da ya ke da nufin gudanarwa, a cewar tuhumar.
Shugaban Amurka Joe Biden da shugaban Ukraine Volodymyr Zelenskyy za su rattaba hannu kan wata yarjejeniyar tsaro ranar Alhamis, yayin da za su gana a Italiya a gefen taron kolin kungiyar kasashe bakwai masu karfin tattalin arziki a duniya.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.