Mutanen 19 da suka fito daga rukuni daban-daban da shugaban Amurka Joe Biden ya karrama a ranar Juma'a saboda yin abin da Fadar White House ta kira a tsayin wadanda suka taka muhimmiyar rawa wajen bada gudunmawa a bangarori daban-daban, da tsaron Amurka da wasu muhimman ayyuka ga al'umma.
Amurka za ta bayar da kusan dala miliyan 55 don magance matsalar jin-kai a Burkina Faso, in ji jami’ar bayar da agaji ta Amurka Samantha Power a ranar Alhamis, a cewar wata sanarwa da Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters ya gani.
A ranar Talata ne aka yanke wa Changpeng Zhao, tsohon shugaban kamfanin Binance, hukuncin zaman gidan yari na tsawon watanni hudu, bayan da ya amsa laifinsa na keta dokokin Amurka kan safarar kudade a babbar kasuwar hada-hadar kudi ta duniya.
Sojojin kasar Mali sun kashe Abu Huzeifa, kwamandan kungiyar Da'ish a yammacin Afirka, a wani gagarumin farmaki da suka kai a yankin Menaka da ke arewacin kasar, a cewar sanarwar da hukumomin Malin suka karanta a gidan talabijin din kasar a ranar Litinin din nan.
Cikin wata sanarwar hadin gwiwa da gwamnatocin Burtaniya da Amurka suka fitar ta yi Allah wa dai da kashe-kashen fararen hula da aka yi a kasar Burkina Faso.
Yarima Harry da matarsa Meghan za su ziyarci Najeriya a watan Mayu don tattaunawa kan wasannin Invictus, wanda ya kirkira don taimakawa tsoffin sojoji da wadanda ke kan aiki masu raunuka don su samu lafiya, in ji wani jami'in Najeriya a ranar Lahadi.
Mahaukaciyar guguwar ta halaka mutum hudu a jihar Oklahoma da ke Amurka tare da barin dubbai da rashin wutar lantarki a Lahadin da ta gabata bayan barkewar wani mummunan yanayi da ya rusa wasu gine-gine a tsakiyar wani gari na karkara tare da raunata akalla mutum 100 a fadin jihar.
Yayin da dalibai a fadin Amurka ke ci gaba da zanga zangar nuna adawa da yakin Isra'ila a Gaza, wasu sun yi Allah wadai da shugabannin Jami'ar Columbia da ke New York saboda kira wa masu zanga zangar jami'an tsaro a makon da ya wuce.
Amurka na shirin janye wasu dakarunta na wucin gadi daga kasar Chadi, a cewar jami'an Amurka a ranar Alhamis, matakin da ya zo kwanaki kadan bayan da Washington ta amince da janye sojojinta daga makwabciyarta Nijar.
Babban jami’in gudanarwa na TikTok ya fada a ranar Laraba cewa kamfanin sadarwar na sa ran samun nasara a kalubalantar dokar toshe manhajar da Shugaba Joe Biden ya sanya wa hannu wadda ya ce za ta hana yada gajerun bidiyon da Amurkawa miliyan 170 ke
Kawo yanzu dai babu wani mataki na karshe kan ko dukkan sojojin Amurka za su fice daga Nijar da Chadi ko kuma a'a, kasashen Afirka biyu da ke da muhimmanci ga kokarin da sojoji ke yi na dakile kungiyoyin masu tsattsauran ra'ayi a yankin Sahel.
Wasu jami'an Amurka biyu sun shaida wa kamfanin dillacin labarai na Reuters a ranar Talata cewa Amurka na shirin bayar da tallafin soji na dala biliyan 1 ga Ukraine, wanda shi ne na farko da za a samu daga kudirin dokar Ukraine da Isra'ila da ba a sanya wa hannu ba tukunna.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.