Yemi Mobolade, dan Najeriya ne kuma dan kasuwa wanda bashi da kwarewa a harkar siyasa, ya zama bakar fata na farko da aka taba zaba a matsayin Magajin Garin Colorado Springs bayan da yayi nasara akan Wayne Williams da daren Talata a zagayen zaben da aka yi a birnin.
Tawagar jami'an da aka kai wa hari ranar Talata a garin Ogbaru na jihar Anambra ta kunshi ‘yan Najeriya guda tara, ciki har da ma’aikatan ofishin jakadancin Amurka a Najeriya biyar da kuma jami’an ‘yan sandan Najeriya hudu.
Amurka ta sha alwashin hana wasu 'yan Najeriya damar shiga kasarta, sakamakon rawar da suka taka wajen yi wa dimokaradiyya zagon kasa a babban zaben kasar na 2023 da aka gudanar.
Sakatariyar Baitul Malin Amurka, Janet Yellen, ta yi gargadin cewa idan har ba a fadada damar karbar bashin ba, nan da farkon watan Yuni gwamnati za ta rasa kudaden da za ta kashe.
Kotu ta umurci Tsohon shugaban Amurka Donald ya biya matar da aka tabbatar ya yi ci zarafinta ta hanyar neman yin lalata da ita shekaru da dama da suka wuce, lamarin da Trump ya sha musantawa a baya.
Zababben shugaban Najeriya, Bola Tinubu, da Dokta Ngozi Okonjo-Iweala, babbar darakta a Cibiyar kasuwanci ta duniya, sun shiga jerin mutane 100 da suka fi tasiri a duniya na shekarar 2023 da Mujallar Time ta fitar.
Ana ci gaba da maida martani game da tuhumar Donald Trump a Amurka inda kawuna suka rabu, wannan dai shi ne karon farko da ake tuhumar wani tsohon shugaba a Amurka.
Masu taimaka wa alkali yanke hukunci na Manhattan (birnin New York) sun tuhumi Donald Trump kan kudin toshiyar baki da aka biya Stormy Daniel.
Shugaba Joe Biden ya bude taron koli na Dimokuradiyya karo na biyu a jiya Laraba, inda ya yi alkawarin cewa Amurka za ta kashe dala miliyan $690M a shekara mai zuwa domin bunkasa shirye-shiryen dimokradiyya a fadin duniya.
Mataimakiyar shugaban kasar Amurka, Kamala Harris, za ta gana da 'yan kasuwa mata na kasar Ghana a yau Laraba, don tattaunawa kan karfafa tattalin arziki da jagoranci,
A yau ne wata kotu a Amurka ta yanke wa wani dan Najeriya mai suna Solomon Ekunke Okpe, dan shekaru 31, hukuncin daurin shekaru hudu da wata daya a gidan yari, bisa samunsa da hannu a wata kungiyar masu aikata laifuka ta yanar gizo.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.