Tsohon shugaban kasar Amurka Donald Trump ya kai karar gidan talabijin na CNN bisa zargin bata masa suna, ya kuma nemi a biya shi diyyar fiye da dala 75,000 da kuma diyya ta dala miliyan 475, a cewar wata karar da aka shigar a yau litinin, kamar yadda CNN ta rawaito.
Mazauna jihar Florida sama da miliyan biyu ne hukumomi suka ba umarnin su bar gidajensu yayin da guguwar Ian ke kusantar yankin.
Hukumomin Amurka sun kwashe shekaru suna son a dawo da shi Amurka domin fuskantar shari’a kan laifukan leken asiri.
Hukumar NDLEA mai yaki da safaran miyagun kwayoyi ta Najeriua ta kama wasu masu safaran muggan kwayoyi da hodar iblis ko cocaine da yawansa ya kai na tan 1.8, ko kwatankwacin kilogram 1855 a birnin Lagos.
Guguwar Fiona ta afkawa gabar tekun Puerto Rico da ke kudu maso yamma a ranar Lahadi yayin da ta haifar da zabtarewar kasa, ta kuma kifar da na'urar wutar lantarki sannan ta tsaga kwalta.
Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta karrama Deborah Samuel dalibar da ta gamu da ajalinta a kwalijin ilimi ta Shehu Shagari da ke Sokoto a hannun wadansu masu tsattsauran ra’ayi.
Mako guda kafin wa’adin tsohon shugaban Amurka Donald Trump ya kare a watan Janairun bara, ‘yan jam’iyyar Republican 10 a majalisar wakilai sun bi sahun gaba daya ‘yan Democrat wajen kada kuri’ar tsige shi saboda tada tarzoma da aka yi a ranar 6 ga watan Janairu a ginin majalisar dokokin Amurka.
An fara zaben masu taya alkali ne yau litinin a shari'ar da gwamnatin tarayya ke wa R. Kelly a garinsa na Chicago, inda shahararran mawakin na R&B ke fuskantar tuhuma kan zarginsa da yin danne gaskiya a shari'ar da aka masa kan aikata lalata a jihar a shekara ta 2008.
Wakiliyar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya, Ambasada Linda Thomas-Greenfield ta yi kira ga Rasha da ta daina dora wa wasu alhakin hare-haren ba gaira ba dalili da ta ke kaiwa kasar Ukraine.
Tsohon shugaban kasar Amurka Donald Trump ya ce jami'an hukumar binciken manyan laifuka ta FBI sun kai samame a gidansa na Mar-a-Lago da ke Palm Beach a jihar Florida.
Jiya Lahadi ‘yan sanda a jihar New Mexico da ke Amurka sun nemi taimakon jama’a wajen gano wata mota da ake nema a bincikensu na harbe wasu Musulmi hudu har lahira wadanda aka kashe a Albuquerque cikin watannin tara da suka gabata da masu bincike suka yi imanin suna da alaka.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.