‘Yan sanda a Nepal sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa, wani jirgin saman fasinja ya rikito yayin da yake kokarin tashi a babban birnin kasar, Kathmandu, inda aka yi nasarar ceto matukin daga tarkacen jirgin dake ci da wuta, saidai dukkanin mutane 18 din dake cikin jirgin sun hallaka