Ma’aikatar tsaron jamhuriyar Nijar ta tabbatar da mutuwar sojojin kasar kimanin 5 sanadiyar hatsarin mota a dai dai lokacin da wani harin ta’addancin da aka kai a madatsar Kandaji da ke jihar Tilabery ya hallaka wasu sojoji 7, sannan wasu 7 suka ji rauni.
Akalla sojojin Nijar goma ne aka kashe a wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a yankin kudu maso yammacin kasar da safiyar Alhamis, kamar yadda wasu majiyoyin tsaro uku suka shaida wa kamfanin dillancin labaran Reuters.
Wasu majiyoyin jami’an tsaro biyu sun ce Sylvain Itte ya ba Nijar ta jirgin sama, labarin da daga bisani ofishin shugaban Faransa dake birnin Paris ya tabbatar.
Ziyarar masu yawon bude ido zuwa tsaunukan Maghreb a baya ta kasance wata kafar samun kudaden shiga da ayyukan yi a yankin da ke fama da fatara.
Cece-kuce ya barke bayan da wasu 'yan jam’iyyar PNDS na kusa da tsohon shugaba Issouhou Mahamadu suka fara zagaya jihohin Nijar don tsara gangamin goyon bayan gwamnatin sojan kasar, lamarin da magoya bayan Bazoum ke kallo a matsayin wanda ke gaskanta zargin hannun Issouhou a juyin mulkin watan Yuli.
Shugaban Faransa Hukumomin mulkin sojan Nijar da jami’an fafutuka sun maida martani bayan da shugaban Faransa ya bayyana shirin dauke jakadan kasar daga birnin Yamai zuwa gida.
Sojojin Nijar sun yi maza sun yi lale marhabin da wannan sanarwa ta Macron wacce suka kwatanta a matsayin “sabon babin ‘yartar” da kasarsu.
Wannan shi ne karo na biyu da tsohon shugaban na Nijar yake bayyana matsayinsa a game da abubuwan da ke wakana a kasar bayan da sojoji suka ba da sanarwar juyin mulki.
Gwamnatin kasar Ghana ta sanar da karin fiye da sittin cikin dari a farashin da take sayen cocoa daga hannun manoman kasar, a kokarinta na neman shawo kan matsalar safarar cocoa zuwa wasu kasashen da ke makwabtaka.
Hukumomin mulkin sojan Jamhuriyar Nijar sun tisa keyar wasu mukarraban hambararriyar Gwamnatin kasar zuwa gidajen yari daban-daban a jihohin Tilabery da Yamai, yayin da aka ba da sanarwar kafa wata sabuwar hukumar yaki da cin hanci da farautar mahandama dukiyar kasa.
Hambararren shugaban Nijar Mohamed Bazoum ya shigar da sojojin da suka yi juyin mulki kara a kotun ECOWAS/CEDEAO sakamakon zargin tsare shi da iyalinsa ba akan ka’ida ba.
Wasu ‘yan siyasa daga jam’iyyar Democrat a Amurka sun bukaci sakataren harkokin wajen Amurka da jakadiyar Amurka a Majalisa Dinkin Duniya su yi amfani da damar babban taron Majalisar Dinkin Duniya don tuntubar shugabanin kasashen CEDEAO kan bukatar sassauta takunkumin da kungiyar ta kakaba wa Nijar.
Domin Kari