Ministan ciniki da masana'antu, Kobena Tahir Hammond, ya sanar da wani muhimmin mataki da gwamnatin Ghana ta dauka na samar da dokar hana shigowa da kayayyaki sama da 20, ciki har da shinkafa da wasu kayayyakin da ake amfani da su a Ghana.
Akalla mutum 573 cikin 11,640 da aka tabbatar sun kamu da cutar a Najeriya sun mutu tun bayan barkewarta a watan Disambar 2022.
Amurka ta gargadi Ghana da cewa idan har ta kuskura ta amince da dokar hana luwadi da madigo, to dangantakar kasuwanci da zuba jari tsakaninsu za ta yi tsami.
Shugaban Majalissar Sojojin juyin mulkin Jamhuriyar Nijar, Janar Abdourahamane Tchiani na ziyarar aiki ta wuni 1 a kasashen Mali da Burkina Faso a wannan Alhamis 23 ga watan Nuwamba.
A ranar Talata ne akasarin ‘yan majalisar dokokin Afirka ta Kudu suka kada kuri’ar amincewa da kudirin rufe ofishin jakadancin Isra’ila tare da yanke huldar diflomasiyya har sai Isra’ila ta amince da tsagaita bude wuta a Gaza.
Hukumomin Mulkin sojan Jamhuriyar Nijar sun bayyana rashin jin dadi game da hukuncin kotun kasashen yammacin Afrika rainon Faransa UEMOA ta yanke dangane da bukatar janye takunkumin da kungiyar ta kakaba wa Nijar din da na ECOWAS a washe garin juyin Mulkin 26 ga watan Yuli.
Ci gaba da rufe iyakokin Najeriya da Jamhuriyar Nijar sakamakon takunkumin kungiyar ECOWAS na ci gaba da haifar da illa ga tattalin arzikin Najeriya musamman arewa maso yammacin kasar.
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya na ziyara a Jamus domin halartar taron hadin-gwiwar Kungiyar Kasashen nan 20 masu Karfin Tattalin Arziki ta G20 da Afirka.
Shugaba Tinubu ya kuma jinjinawa Shugaba George Weah da ya amince da shan kaye, matakin da ya ce zai taimaka wajen kaucewa ta da hargitsin siyasa.
Shugaba George Weah na Laberiya ya sha kaye a zagaye na biyu na zaben shugaban kasar da aka gudanar a ranar Talata, bayan da sakamakon farko ya nuna cewa abokin hamayyarsa Joseph Boakai ne ke kan gaba da mafi rinjayen kuri'un da aka kada.
Dakarun tsaron jamhuriyar Nijar sun yi nasarar hallaka ‘yan ta’adda sakamakon wata arangamar da suka yi a gundumar Sanam ta jihar Tilabery. Lamarin ya faru ne ranar Alhamis 16 ga watan Nuwamba jim kadan bayan da ‘yan bindigar suka kona wata makarantar boko a kauyen Maichilmi.
Gwamnatin Ghana ta yi hasashen cewa tattalin arzikin kasar zai kai Ghana-Cedi (GHC) Triliyan 1 (kimanin dala biliyan $84) na GDP a shekarar 2024, yayin da ta janye wasu haraji domin rage wa al’umma radadin matsalar tattalin arziki da kasar ke fuskanta.
Domin Kari