Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kasashen Yammacin Afirka Na Kokarin Shawo Kan Cutar Mashako


Ana yi wa wani jariri rigakin cutar mashako
Ana yi wa wani jariri rigakin cutar mashako

Akalla mutum 573 cikin 11,640 da aka tabbatar sun kamu da cutar a Najeriya sun mutu tun bayan barkewarta a watan Disambar 2022.

Hukumomi a kasashen Yammacin Afirka da dama na kokarin shawo kan cutar mashako da ta barke a yankin, ciki har da Najeriya, inda wani babban jami’in lafiya ya fada a ranar Alhamis cewa an yi wa miliyoyin mutane rigakafi, domin cike gibin rigakafin cutar.

Akalla mutum 573 daga cikin 11,640 da aka tabbatar sun kamu da cutar a Najeriya sun mutu tun bayan barkewarta a watan Disambar 2022.

Ko da yake, jami’ai sun kiyasin cewa adadin a yanzu ya ragu saboda samar da ingantattun matakan jinya.

A Jamhuriyar Nijar kuma da ke makwabtaka da Najeriya, mutum 37 ne suka mutu cikin mutum 865 da suka kamu da cutar ya zuwa watan Oktoban da ya wuce, yayin da a kasar Guinea aka ba da rahoton mutuwar mutum 58 daga cikin 497 da suka kamu tun bayan barkewar cutar a watan Yuni.

Ya zuwa yanzu dai an samu rahoton kamuwa da cutar mai saurin yaduwa a jihohi 20 cikin 36 na Najeriya.

A Najeriya, kashi 42 cikin 100 na yara ‘yan kasa da shekaru 15 ne kawai ke samun cikakkiyar kariya daga kamuwa da cutar ta mashako, a cewar wani bincike na gwamnati.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG