A yau Juma'a ne babbar kotun kasar Nijar ta dage rigar kariyar hambararren shugaban kasar Nijar, Mohamed Bazoum, lamarin da zai bada damar a yi masa shari'a bayan hambarar da shi a watan Yulin 2023.
A ranar Alhamis kwamitin sulhun majalisar dinkin duniya ya zarta da kudurin da ya nemi dakarun kar ta kwana na Sudan da su gaggauta daina kawanyar da su ke yi a babban birni daya tilo a yankin Arewacin Dafur da ba ta da iko da shi, kuma wurin da aka ruwaito cewa mutane sama da miliyan suka fake.
Sanarwar da Tshisekedi ya fitar ta ce, jirgin ruwan da aka kera a cikin gida ya kife da yammacin ranar Litinin a lardin Maï-Ndombe da ke gabar kogin Kwa
Hukumomin mulkin sojan jamhuriyar Nijar sun tsaurara matakai da nufin taka burki ga masu amfani da nufin saka tsari a kafafen sadarwa bayan da suka ce wasu na fakewa da wadanan hanyoyi don cin zarafin mutane.
Har yanzu dai babu wanda ya dauki alhakin kai harin, wanda shi ne na farko kan jami’an tsaron dake kare bututun mai.
A karon farko an gano cewa wasu mutane a nahiyar Afirka na amfani da muguwar kwayar Nitazenes dangin opiod, a cewar wani rahoto da kungiyar yaki da manyan laifuka ta kasa da kasa mai zaman kanta da ake kira Global Initiative Against Transnational Organized Crime ta fidda.
Ta yiwu ranar Alhamis kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya zai kada kuri'a kan wani kuduri da Birtaniyya ta gabatar da daftarinsa.
A yayinda aka fara samun saukar ruwan sama a albarkacin damunar bana a sassan jamhuriyar Nijar, hukumar kula da aiyukan agajin gaggawa ta sanar cewa ambaliyar ruwa ta yi sanadin mutuwar mutane fiye da 10 yayin da daruruwan gidaje suka ruguje
Gwamnatin Nijar ta sanar da daukar matakan da suka dace domin karbo manyan jami’anta da hukumomin Benin suka kama.
Mataimakin shugaban kasar Malawi, Saulos Chilima, ya mutu a wani hatsarin jirgin sama, kamar yadda shugaban kasar ya bayyana a ranar Talata, bayan da masu bincike suka gano tarkacen jirgin a wani dajin da ke cike da hazo.
Sojoji na duba tsaunuka da dazuzzuka da ke kusa da wani birni a arewacin Malawi bayan da wani jirgin saman soja dauke da mataimakin shugaban kasar ya bace a yankin a ranar Litinin, in ji shugaban kasar Lazarus Chakwera.
Kamfanin dillancin labaran Reuters ya ce rikicin ya barke ne a ranar Asabar a garuruwan Abudwaq da Herale da ke yankin Galmudug kan wuraren kiwo da wuraren ruwa.
Domin Kari