Rasuwar tsohon shugaban kasar Mali Ibrahim Boubacar Keita mako guda bayan takaddamar da ta kunno kai tsakanin ECOWAS da gwamnatin rikon kwaryar ta Mali ta janyo aza ayar tambaya dangane da makomar takunkumin da kungiyar ta kakabawa Mali.
A jamhuriyar Nijer, masu aikin jigila sun koka a game da tsayawar harakoki bayan da hukumomin sufuri suka rufe iyakar kasar da makwabciyarta kasar Mali.
Masana sha’anin tsaro sun bayyana fargaba akan yiyuwar fuskantar koma baya a game da yaki da ta’addanci a yankin Sahel sakamakon matakin rufe iyakoki da kungiyar ECOWAS ta yi saboda saba alkawalin shirya zabe da gwamnatin rikon Mali ta yi.
Gwamnatin jamhuriyar Nijar ta kara jaddada aniyar ci gaba da bibiyar shari’ar nan ta mutanen da ake zargi da handame kudaden makamai a ma’aikatar tsaron kasar bayan bayyanar wasu takardun dake nunin hukumomin Nijar sun janye daga wannan shari’a.
Hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta gabatar da wasu mutane da ta kama dauke da kilogram (kg) sama da 200 na hodar iblis da aka loda a motar magajin garin Fachi dake jihar Agadez a Nijar a lokacin da suka yi kokarin ketarawa zuwa kasar Libya.
A Jamhuriyar Nijar, wata kungiyar Fulani ta bayyana rashin jin dadinta dangane da yadda ake zargin Fulani da hannu a ayyukan ta’addanci da na ‘yan bindigar da suka addabi jama'ar wasu yankunan kasar saboda haka suka bukaci hukumomi su gagauta daukan matakai don kaucewa barkewar rikicin kabilanci.
Lauyar dake kare ‘yan Rwandar nan da gwamnatin Nijar ta kora daga kasar ta bayyana damuwa a game da abinda ta kira rashin mutunta alkawuran da kasar ta dauka a yarjejeniyar da suka cimma da MDD akan batun bai wa wadanan mutane mafaka.
Hukumomin jamhuriyar Nijar sun kori wasu ‘yan Rwanda daga kasar saboda dalilan da aka bayyana a matsayin na diflomasiya, sai dai wasu ‘yan rajin kare hakkin dan adam na ganin alamar keta hakkin dan adam a wannan lamarin.
Kungiyoyin ‘yan kasuwar Jamhuriyar Nijar sun bayyana farin ciki bayan da shugaban hukumar Douane ya umurci ma’aikatansa su dakatar da matsawa ‘yan kasuwa game da takardar izinin wucin gadin fiton kaya.
‘Yan bindiga sun kai tagwayen hare-hare a wasu tashoshin bincike a garin Makalondi dake jihar Tilabery iyaka da Burkina Faso inda suka hallaka jami’an tsaro tare da kona motoci sannan suka arce da wasu motocin ‘yan sanda.
A yayin da rundunar tsaron Faransa ta bada sanarwar kashe shugaban reshen kungiyar IS a yankin Sahara Soumana Boura a wani harin hadin gwiwa da dakarun tsaron jamhuriyar Nijer, masana sha’anin tsaro na da ra’ayoyi mabambanta dangane da tasirin wannan nasara a yaki da ta’addanci a yankin Sahel.
A jamhuriyar Nijer kungiyar AJSEM da hadin guiwar UNESCO sun shirya wani taro domin fadakar ‘yan jarida akan bukatar mutunta ‘yancin ‘yan cirani ta yadda za a daina amfani da kalaman da ke kama da na cin zarafin bakin haure a yayin bada labari
A Jamhuriyar Nijar shugabanin al’umar karkarar Lahari dake yankin Diffa sun bayyana damuwa dangane da yanayin da ayyukan hakar man fetur suka jefa su ciki inda gurbacewar muhalli ta shafi ayyukan noma da kiwo.
A jamhuriyar Nijar shugabannin al’umar karkarar Lahari dake yankin Diffa sun bayyana damuwa dangane da yanayin da ayyukan hakar man fetur suka jefa su ciki inda gurbacewar muhalli ta shafi ayyukan noma da kiwo, saboda haka suka bukaci hukumomin kasar su dubi wannan al’amari kafin abin ya tsananta.
A jamhuriyar Nijar hukumomin kiwon lafiya sun bada sanarwar dakatar da tallafin kudaden tiyatar haifuwa da aka saba yiwa mata kyauta sakamakon wasu dalilai masu nasaba da tsarin aikin, amma kuma za a ci gaba da tsarin bada magani kyauta ga mata masu juna biyu da yara kanana.
A jamhuriyar Nijar wasu ‘yan majalisar dokokin kasar sun zargi kakakin majalisar Alhaji Seini Oumarou da taka doka sakamakon rashin ba su damar sauraren Ministan tsaro da takwaransa na cikin gida a game da abubuwan da suka faru a ranar 27 ga watan Nuwamba da ya gabata a garin Tera.
Hukumar yaki da cin hanci a Jamhuriyar Nijar ta kaddamar da wani aikin zuba ido akan ayyukan ‘yan sandan kula da zirga-zirga da nufin tantance zahirin abubuwa irin na cin hanci da ake zargin su da aikatawa.
Jami’an tsaro sun kama kusoshin wata kungiyar fafutika cikinsu har da wani dan kasar Faransa.
Hadin gwiwar sojojin jamhuriyar Nijar da takwarorinsu na Burkina Faso sun yi nasarar wargaza wani sansanin 'yan ta'adda dake kan iyakar kasashen biyu, lamarin da ya ba su damar kashe 'yan ta'adda kusan 100 tare da kama makamai da babura fiye da 200.
Hukumomin jamhuriyar Nijar sun kama shugaban kungiyar hadin kan al’umar jihar Tilabery Amadou Harouna Maiga bayan da ya yi wasu kalamai dangane da zanga-zangar nan ta matasan da suka datsewa ayarin motocin sojan Faransa hanya a garin Tera a ranar 27 ga watan November 2021.
Domin Kari