Hukumomin Nijer sun yi tur da yadda Rasha ta yi watsi da dokokin kasa da kasa ta hanyar mamayar Ukraine, a cewarsu alama ce da ke nuna girman barazanar da kasashe masu karamin karfi ke fuskanta daga wadanda ke da ra’ayin amfani da karfin soja don cimma gurinsu.
Ministan tsaron Faransa da abokiyar aikinsa ta harakokin waje sun yi rangadi a Jamhuriyar Nijar inda aka tattauna akan batutuwan da suka hada da tsaro da ayyukan ci gaban al’umma a wani lokacin da rundunar Barkhane ke ci gab da kammala nade tarkacenta daga Mali zuwa jamhuriyar Nijar.
Kasashen Chadi da Nijar sun yi kiran Mali ta koma kan kujerarta a kungiyar G5 Sahel domin ci gaba da yakin hadin-gwiwar da takwarorinta ke kafsawa da kungiyoyin ta’addancin yankin Sahel.
Rundunar mayakan Jamhuriyar Nijar ta sanar cewa dakarun tsaro sun hallaka gomman ‘yan ta’adda a tare da wargaza ma’ajiyar kayayyakin ‘yan ta’adda a yammacin kasar banda wasu nasarorin da tace an samu a sauran yankunan dake fama da matsalolin tsaro.
Yayin da dumamar yanayi ke cigaba da illa a sassan duniya, wani taro da ake yi a Jamhuriyar Nijer zai yi bitar yadda abin ke shafar Afurka ta Yamma da kuma yadda za a dau matakin kare muhalli.
Yayin da kasashen Nijer da Benin ke fama da matsalar 'yan bindiga, makwabtan kasashen sun yanke shawarar hada karfi da karfe wajen tinkarar miyagun.
Wani bincike da aka gudanar a kasashen yankin Sahel wanda kuma aka gabatar da rahotonsa a taron kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya a karshen makon jiya ya gano cewa mata da yara kanana sun fi kowa dandana kuda a tashe tashen hankulan da ake fama da su.
Ma’aikatar kudin Jamhuriyar Nijar ta fitar da sakamakon wucin gadi na binciken da aka gudanar domin kididdige ma’aikatan gwamnatin kasar da nufin tantance halattattun ma’aikata da na bogi.
Duk da cikar wa'adin jigilar maniyyata aikin Hajji na bana a yau Laraba, ga dukkan alamu sauran maniyyatan Nijer sama da 1000 za su iya samun Hajjin saboda Saudiyya ta kara ma Nijer lokaci, a cewar hukumomi.
Jami’an kare hakkin jama’a da ‘yan rajin kare dimokradiya sun yi na’am da matakin dage takunkumin da kungiyar ECOWAS ta kakaba wa kasar Mali a washe garin juyin mulkin da ya kifar da shugaba Ibrahim Boubakar Keita daga karagar mulki.
A jamhuriyar Nijer wasu daga cikin maniyatan aikin Hajji sun fara komawa garuruwansu bayan la’akari da cewa zai yi wuya a kai su kasar Saudiya kafin ranar 6 ga watan Yuli, duk da cewa mahukuntan Nijer sun sha alwashin kwashe dukkan mutanen da suka samu takardar Visa.
A Jamhuriyar Nijar an shiga halin dambarwa bayan da majalisar addinin Islama a kasar ta ayyana ranar Lahadi 10 ga watan Yuli a matsayin ranar da za a yi bukukwan babbar sallar a maimakon ranar asabar.
Yayinda har yanzu kashi 2 daga cikin 3 na maniyatan hajin bana ke jiran zuwan jiragen da zasu kwashe su don zuwa kasa mai tsarki hukumomi sun bada tabbacin daukan dukkan matakan da zasu ba alhazan damar safka kasar Saudia kafin wa’adin rufe filayen jiragen saman Madina da na Jidda ya cika.
Babban kwamandan rundunar tsaro ta Amurka a nahiyar Afrika wato AFRICOM General Stephen J. Townsend ya yi rangadi a Jamhuriyar Nijer inda suka tantauna da shugaba Mohamed Bazoum game da batutuwan da suka shafi sha’anin tsaro da yaki da ta’addanci a kasar da ma yankin sahel baki daya.
Shugaban kasar Nijar Mohamed Bazoum na shirin fara rangadi a jihar Diffa a gobe asabar 25 ga watan Yuni da nufin duba halin da ake ciki shekara guda bayan kaddamar da ayyukan mayar da ‘yan gudun hijira garuruwansu na asali.
Majalisar dokokin Jamhuriyar Nijar ta amincewa gwamnatin kasar ta soma zartar da dokar hukuncin biyan tara ga mutanen da aka kama da laifin cin zarafi ko yiwa wani kazafi ta yanar gizo a maimakon hukuncin zaman wakafi da aka saba yankewa irin wadanan mutane a can baya
Gwamnatin rikon kwaryar Mali ta tabbatar da rasuwar fararen hula sama da 100 sakamakon harin da ‘yan ta’adda suka kai a wasu kauyukan tsakiyar kasar a karshen mako sai dai wani dan siyasar yankin da abin ya faru na cewa yawan wadanda aka kashe ya haura 200.
Kasashen duniya sun yi bukin tunawa da ranar yaki da cutar amosanin jini, daya daga cikin cututukan da suka fi wahalar da jama’a a kasashe masu tasowa.
Domin Kari