A wani yunkurin samar da kudaden daukar dawainiyar al’amuran gudanar da sha’anin mulkin gwamnatin rikon kwaryar Jamhuriyar Nijar, gwamnatin mulkin soji ta kafa wata gidauniya da nufin tattara gudummawar kudade daga ‘yan kasar na ciki da waje.
A Jamhuriyar Nijar mambobin kungiyar Mata Masu Dubara (MMD) sun yi gangami a harabar babban bankin kasashen Afrika ta yamma rainon Faransa (BCEAO) don matsa lamba wa shugabannin bankin su mayar wa kasar kudaden ajiyarta wadanda takunkumin kungiyar UEMOA ya rutsa da su sakamakon juyin mulki.
Wani alkalin kotun Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar ya bada belin ‘yar jaridar nan Samira Sabou, bayan da ta shafe kwanaki 4 a hannun ‘yan sandan farin kaya.
Rukunin farko na sojojin Faransa sun fice daga Nijar zuwa gida bayan shafe watanni sama da 2 ana kace -nace akan wannan batu da ya haifar da tankiyar diflomasiyya tsakanin sojojin juyin mulkin 26 ga watan Yuli da hukumomin Faransa.
A jamhuriyar Nijer ‘Yar jaridar nan mai fafutuka ta yanar gizo, Samira Sabou da ta yi batan dabo a karshen watan Satumba ta bayyana a ranar Asabar din da ta gabata.
Ko da yake ba'a bayyana dalilan daukan wannan mataki a hukumance ba ‘yan rajin kare hakkin masaya na ganin abin a matsayin wata hanyar samar da wadatar gas ga al’ummar kasar ne.
Kungiyar M62 ta gabatar da takarda a ofishin ministan harkokin wajen Nijar akan bukatar maka tsohon Shugaba Issouhou Mahamadou a kotun kasa da kasa ta ICC, saboda zarginsa da aikata miyagun laifuka da zama silar aika-aikar ‘yan ta’addan da ake fama da su, abinda makusantansa ke cewa zancen banza ne.
Hukumomin Jamhuriyar Nijar sun ayyana zaman makokin kwanaki 3 daga ranar 3 ga watan Oktoba da nufin nuna alhinin rasuwar wasu sojojin kasar akalla 29, bayan wani hari da ‘yan ta’adda suka kai a ranar Litinin a kan iyakarta da Mali.
Shugaban Majalisar sojojin juyin mulkin Jamhuriyar Nijar Janar Abdourahamane Tchiani ya aike wa shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu sakon taya murnar zagayowar ranar cika shekaru 63 da samun ‘yancin kan Najeriya.
Kungiyoyin kare hakkin ‘yan jarida a Jamhuriyar Nijar sun bayyana damuwa bayan da wata ‘yar jarida kuma shugabar kungiyar masu fafutika ta yanar gizo Samira Sabou ta yi batan dabo a yammacin ranar Asabar din da ta gabata.
Ma’aikatar tsaron jamhuriyar Nijar ta tabbatar da mutuwar sojojin kasar kimanin 5 sanadiyar hatsarin mota a dai dai lokacin da wani harin ta’addancin da aka kai a madatsar Kandaji da ke jihar Tilabery ya hallaka wasu sojoji 7, sannan wasu 7 suka ji rauni.
Cece-kuce ya barke bayan da wasu 'yan jam’iyyar PNDS na kusa da tsohon shugaba Issouhou Mahamadu suka fara zagaya jihohin Nijar don tsara gangamin goyon bayan gwamnatin sojan kasar, lamarin da magoya bayan Bazoum ke kallo a matsayin wanda ke gaskanta zargin hannun Issouhou a juyin mulkin watan Yuli.
Shugaban Faransa Hukumomin mulkin sojan Nijar da jami’an fafutuka sun maida martani bayan da shugaban Faransa ya bayyana shirin dauke jakadan kasar daga birnin Yamai zuwa gida.
Wannan shi ne karo na biyu da tsohon shugaban na Nijar yake bayyana matsayinsa a game da abubuwan da ke wakana a kasar bayan da sojoji suka ba da sanarwar juyin mulki.
Hukumomin mulkin sojan Jamhuriyar Nijar sun tisa keyar wasu mukarraban hambararriyar Gwamnatin kasar zuwa gidajen yari daban-daban a jihohin Tilabery da Yamai, yayin da aka ba da sanarwar kafa wata sabuwar hukumar yaki da cin hanci da farautar mahandama dukiyar kasa.
Hambararren shugaban Nijar Mohamed Bazoum ya shigar da sojojin da suka yi juyin mulki kara a kotun ECOWAS/CEDEAO sakamakon zargin tsare shi da iyalinsa ba akan ka’ida ba.
Domin Kari