Alkalin babbar kotun tarayyar Najeriya Justice Gabriel Kolawale, ya janye daga wata shari’a da ta shafi tsohon mai bada shawara kan tsaro Kanal Sambo Dasuki.
A kokarin taimakawa alhazan Najeriya su saukar da aikin ibadar wannan shekarar hukumar alhazai ta bukaci Saudiya ta kara cibiyoyin daukar shaidar tambarin yatsun mutum kazalika an kira gwamnati ta ragewa alhazan farashin dala
Sanarwar da kakakin fadar shugaban Najeriya Malam Garba Shehu ya fitar ta ce shugaban yana iyakar kokarinsa wajen cika alkawuran da ya yi lokacin neman zabe saboda yaki da cin hanci da rashawa da inganta tsaro da kuma habaka tattalin arziki ne shugaban ya sa gaba
Najeriya na ci gaba da bunkasa noma da sarrafa shinkafa, matakin da ya sa har wasu kamfanonin Thailand guda bakwai sun durkushe saboda Najeriya ta daina sayen shinkafarsu
Sa’oi kadan bayan da kotun tarayya ta ba da belin Maryam Sanda, matar da ake tuhuma da kashe mijinta, Bilyaminu Bello a Abuja, babban Birnin Najeriya, masana shari’a sun fara fashin baki kan wannan hukunci.
Jigogin wannan kungiya wadanda suka hada da Attahiru Bafarawa da Ibrahim mantu sun ce makasudin wannan gamayya ta su shine maido da tasirin siyasar da suka ce linzaminta ya kubuce ma 'yan arewa
Hukumar INEC ta Najeriya ta karawa ma'aikatanta girma har zuwa matakin aikin gwamnati na goma sha biyar. Sannan kuma a Jihar Zamfara ana takaddamar tantance Kwamishinan zaben da suke kiki-kakar cewa ba dan asalin jihar ba ne shi yasa ba zasu amince da shi ba.
Babban taron PDP ya caza manyan ‘yan jam’iyyar da nuna babu barin baya da ‘kura da zai shafi tasirin jam’iyyar a zaben shekarar 2019.
An zabi Uche Secondus a matsayin sabon shugaban babbar jam'iyyar adawa a Najeriya, PDP, bayan da aka kammala kidaya kuri'un zaben da aka gudanar jiya Asabar.
Akwai alamu da ke nuna cewa, mai yiwuwa akai ruwa rana a babban taron da jam'iyar PDP mai adawa ke yi a Abuja, bayan da gwamnonin kudu maso kudu suka nuna alamun goyon bayan dan takarar da ya fito daga yankinsu a matsayin dan takarar shugaban jam'iyar.
Hadaddiyar kungiyar matasan arewacin Nigeria ta janye umarnin korar yan Kabilar Igbo daga arewacin kasar, amma ta gitta wasu sharudda.
A wani mataki na ganin an magance matsalolin da masu manyan motoci suke haifarwa, kama daga bata hanyoyi zuwa haifar da hadurra a duk fadin Najeriya, hukumomin kasar na shirin samar da wuraren dakatarwar motocin a sassan kasar.
An Fara jigilar maniyyata hajjin Najeriya zuwa kasar Saudiya domin gudanar da aikin hajjin bana. An bude aikin jigilar ne da alhazan Abuja, babban birnin kasar.
Ana kara samun bayanai kan halin da shugaban Najeriya ke ciki tun bayan da ya tafi jinya a birnin London a watan Mayu, a baya-bayan nan wasu gwamnonin kasar ne suka kai mai ziyara inda suka ce sun sami shugaban cikin yanayi mai kyau.
Yayinda yake jawabi a mijami'ar fadar shugaban kasa dake cikin Aso Villa mukaddashin shugaban Najeriya Farfasa Yemi Osin bajo ya bukaci duk shugabannin mijamiun Najeriya da su yi waje da duk masu halin bera dake tsakaninsu.
Shugabannin jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya na kara ba da tabbacin cewa hukumar da aka amince a kafa ta raya arewa maso gabashin Najeriya da rikicin Boko Haram daidaita za ta fara aiki.
Kwararru a taron kwamitin shugaban Najeriya mai tallafawa Arewa maso Gabas, sun gano cewa gina gidaje nesa da juna a yankunan Borno na samawa ‘yan ta’adda saukin afkawa jama’a.
Shugaban jam’iyyar PDP Sanata Ali Modu Sheriff ya shiga ofis a hedikwatar jam’iyyar ta Wadata Plaza dake Abuja.
Wata kotun tarayyar Najeriya ta yankewa wata mata hukuncin ‘dauri bayan da aka same ta da laifin yunkurin safarar hodar iblis daga Najeriya zuwa Saudiya.
Kungiyar matasa Kristoci masu wanzar da salama da kuma reshen matasa na kungiyar Kristocin Najeriya CAN sun gudanar da taron wanzar da zaman lafiya a birnin Abuja.
Domin Kari