Najeriya na daga cikin kasashen da ke da arziki wanda ya kamata jama'ar ta su more rayuwarsu, sai dai har yanzu alamu na nuna cewa mutane musamman mazauna kauyuka na fama da kishirwa da wasu muhimman ababen more rayuwar.
Dubban katunan zabe da aka yi wa rijista ke jibge a wasu ofisoshin hukumar zaben Najeriya da ba a karba ba, a cewar hukumar INEC.
An dade ana tada jijiyar wuya a Najeriya kan batun kafa masana'antu a wuraren al'umma, abin da wasu lokuta kan kai ga al'umma daukar mataki ko da mummuna ne kamar abinda ya sha faruwa a yankin Naija Dalta.
Wannan na zuwa ne bayan wani hukunci da kotun daukaka kara a Sokoto ta yanke na hana tsohon gwamnan jihar Kebbi Sanata Adamu Aliero da tsohon jagoran majalisar dattawa Sanata Yahaya Abdullahi yin takarar kujerun Sanata a zaben 2023.
Majalisar wakilai ta tarayyar Najeriya ta dukufa ga binciken ayukkan Sojin kasar da manufar kara shiryawa wasu ayukkan a shekara mai zuwa.
A Najeriya alamu na nuna cewa hukumomi tsaron kasar na kara daukar matakai na tabbatar da kawar da matsalolin rashin tsaro da suka zamo kashi-bakin-tulu ga kasar.
Rundunar sojin Najeriya ta ce tana aiki tukuru wajen bin umurnin shugaban kasa na kawar da ayyukan ‘yan ta'adda a ko'ina cikin fadin kasar.
Sakacin gwamnati da al'ummar Najeriya na daga cikin abubuwan da suka kawo bazuwar matsalolin rashin tsaro a Arewa maso Gabas da sauran wurare daban daban.
Dubban ‘yan Najeriya marasa lafiya ne ke cikin adadin marasa lafiya miliyan daya da rabi daga kasashe 42 da ke cin gajiyar ayyukan kula da lafiya kyauta daga likitocin da ke yawo kasashen duniya don bayar da agajin kiyon lafiya.
Yayin da wasu kasashen duniya ke fuskantar kalubale ta fuskoki daban-daban, masana sun ce akwai mafita ga kowane irin kalubale da ake fuskanta a duniya.
Hukumar hana sha da safarar miyagun kwayoyi ta dira kan wasu wuraren shan miyagun kwayoyi ,ta kama matasa maza da mata da yawan su ya kai 28.
‘Yan Najeriya na ci gaba da yin tsokaci akan bukatar mahukunta su rika sanya ido da tabbatar da yin adalci ga dukkan abubuwan da ke faruwa domin kauce wa ci gaba da haifar da matsalolin tashin hankali a kasar.
Hadarin kwale-kwale na ci gaba da lakume rayukan jama'a a Najeriya duk da matakan da mahukunta ke shan alwashin dauka na kawar da aukuwarsu ko magance mace-mace idan aka samu hadarin.
Masu lallura ta musamman sun ce suna fuskantar kalubale wajen tafiyar da lamurran su na yau da kullum saboda rashin kulawa da hakkoki na inganta jin dadinsu.
Masana lamurran tsaro a Najeriya na ci gaba da tsokaci akan yadda ‘yan ta'adda da ake kamawa ke nuna gadara suna bayyana ta'addancin da suka yi, bayan sun shiga hannun hukuma, abinda suke gani da cewa akwai ayar tambaya a ciki.
Yayin da harkokin siyasa suka kankama gadan-gadan a Najeriya, wasu ‘yan kasar na mamakin yadda gwamnatocin siyasa da suka yi mulki suka kasa warware matsalolin rayuwa ga jama'a, tare da nuna fargabar kada gwamnati mai zuwa ta bi sawun ta baya.
A Najeriya, yayin da wasu mayakan kasar ke fagen daga suna fafatawa da abokan gaba, wasu suna can hannu suna fuskantar shari'a akan wasu laifuka da ake tuhumar su akai.
Masana a Najeriya na ganin daga cikin illolin da rashin tsaro ya haifar ga jama'a akwai rashin sanin makomar kananan yara dake gudun hijira, wadanda basu samun ilimi, wanda zai sa su kasance da tsarin rayuwa idan sun girma.
Yayin da shugabannin kasashen duniya ke ci gaba da tsokaci akan yakin da kasar Russia ke yi da Ukraine, Malaman addini sun soma karkata hankulansu akan bukatar jama'a su bada tasu gudunmuwa wajen kawo karshen yakin.
A wasu sassan Najeriya matsalar tsaro na ci gaba da hana jama'a barci da ido biyu rufe, duk da cewa rahotanni na nuna jami'an tsaro na samun galaba akan ‘yan ta'adda a wasu wurare.
Domin Kari