An haifi yaro namiji, a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin Najeriya, wanda ya zo da gangar jiki daya, da kai biyu, idanu hudu, baki biyu da kuma hanci biyu.
Yayin da al'ummomin wasu yankunan Najeriya ke farin ciki a kan matakan da mahukunta suka dauka wadanda suke fatar su kawo sauki ga matsalar rashin tsaro, wasu kuwa fargaba ce ta karu gun su domin suna ganin barayin zasu kwararo yankuan su ne daga yankunan da aka dauki matakan.
Bayanai sun nuna cewa bayan wadanda 'yan bindigar suka kashe hakama sun yi garkuwa da wasu da ba a san adadin su ba.
Bayanai na nuni da cewa hakan na faruwa ne yayin da matsalar ta rashin tsaro ke raguwa a arewa maso yammcin kasar, kamar a yankunan jihar Sokoto.
Daga daya zuwa gomasha biyar ga Jana'irun kowace shekara, gwamnatin Najeriya, kama da ga matakin tarayya har zuwa jihohi, sukan gudanar da bukukuwa na tunawa da sojojin da suka sadaukar da rayukan su wajen ganin kasar ta tsayu da kafafunta.
Yayin da gwamnatin Najeriya ke cewa tana daukar matakai domin bunkasa ayukkan kasuwanci da habaka tattalin arziki, wasu 'yan kasuwa na kokawa akan cewa har yanzu suna fuskantar kalubale da ke yin tarnaki ga kasuwanci da kuma tattalin arzikinsu.
Wasu sarakuna da suka hada da 'yan majalisar Sarkin musulmi na dakon fuskantar hukunci, sakamakon wani kwamiti da gwamnatin Sakkwato ta kafa don gudanar da bincike akan zarginsu da aikata laifuka masu alaka da siyasa.
'Yan Najeriya na ci gaba da kalubalantar gwamnati akan matakan da take cewa tana dauka da zasu kawo karshen matsalolin tsaro, yayin da ake ci gaba da alhinin kisan kiyashi da aka yi wa jama'a a jihar Plateau.
Yayin da wasu jihohi a Najeriya musamman na arewa ke fuskantar kalubale a bangarori daba daban, hukumomi na duniya na ci gaba da kai dauki domin taimakawa jihohin a sassa daban daban na rayuwa.
'Yan bindiga na ci gaba da cin karensu ba babbaka a wasu yankunan arewacin Najeriya duk da kalaman da mahukunta ke yi na cewa suna daukar matakai na magance matsaloin.
Hukumar yaki da sha ko tu'ammuli da miyagun kwayoyi a Najeriya ta hada hannu da sauran jami'an tsaro domin kara tsaftace al'umma daga illolin tu'ammuli da miyagun kwayoyi, yayin da shekara ta 2023 ke bankwana, bukukuwan Kirsimati da sabuwar shekara ke kara matsowa, .
Gwamnatin jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin Najeriya, ta samar da babura dari bakwai da talatin, domin rabawa jami'ansa kai na banga, domin su rika taimakawa jami'an tsaro na hukuma wajen sintiri don yaki da matsalar rashin tsaro.
Al'ummomi mazauna yankunan da ke fama da matsalar rashin tsaro a Najeriya na ci gaba tsokaci tare da nuna mamakin cewa ashe gwamnatin kasar na da jiragen yaki da ke iya hallaka jama'a da yawa, amma ta bar su 'yan bindiga na cin zarafin su.
Yayin da ake bukin ranar masu bukata ta musamman a duniya , masu bukata ta musamman a Najeriya sun ce mutumtawa da aiwatar da dokar kula da hakkokin su da gwamnatin Najeriya ta sanyawa hannu tun shekarar 2019, ne kadai kan iya magance matsalolin da suke fuskanta a rayuwa.
Ci gaba da rufe iyakokin Najeriya da Jamhuriyar Nijar sakamakon takunkumin kungiyar ECOWAS na ci gaba da haifar da illa ga tattalin arzikin Najeriya musamman arewa maso yammacin kasar.
Wasu da ake tuhumar barayin daji ne, sun bayyana cewa bisa ga tilas ne suke aikata ayukkan ta'addanci saboda koda yaushe a daji suke zaune kuma nan ne suke samun abin dogaro da kai, sannan kuma a nan ne ake shirya munanan ayukka da barayin ke gudanarwa.
Rundunar 'yan sandan Najeriya ta tabbatar da kisan mutane biyar tare da kona kayan abinci da abubuwan hawa, a wani hari da 'yan bindiga suka kai da safiyar Litinin a garin Gidan Buwai da ke karamar hukumar Rabah a jihar Sokoto da ke Arewa maso yammacin Najeriya.
Hatsabibin dan bindigar nan da ake kira Dogo Gide ya sha da kyar bayan da sojojin Najeriya suka samu nasarar hallaka wasu manyan 'yan bindiga uku a jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin Najeriya.
Wani batu da ya ja hankalin 'yan Najeriya a kwanannan shi ne na wata daliba da aka kora daga makarantar nazarin kimiyar ayukkan jinya da ungozoma ta jihar Kebbi, da sunan cewa tana badala a dandalin sada zumunta na yanar gizo na Tiktok.
A Najeriya yayin da mahukunta ke kokarin lalubo mafita ga matsalar tsaro, su kuwa 'yan bindiga sai ci gaba suke yi da addabar jama'a ta hanyar kisa da yin garkuwa da su.
Domin Kari