Yanzu Italiya za ta jira tsakanin Ingila ko Denmark wadanda za su kara a ranar Laraba a daya wasan zagayen semi-final.
Wata babbar kotu a Kano, ta yanke hukuncin cewa gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya biya Jaafar Jaafar da kamfanin jaridar Daily Nigerian naira dubu 800 saboda lokaci da aka bata masu da kuma bata masu suna da aka yi.
“Mun samu kira daga ‘yan bindigar, kuma sun tabbatar mana cewa daliban suna cikin koshin lafiya.” Rev. Jangado ya ce.
An ba kwamitin kwana 60 ya kammala aikinsa daga ranar da ya fara zaman farko inda zai mika rahoto da shawarwari kan matakin da ya gwamnati ta dauka.
Rahotannin sun ce nan take aka garzaya da ita asibitin horarwa na ATBU don ba ta taimakon gaggawa.
A ranar Litinin kungiyar gwamnonin jihohin Najeriya ta rungumi matsaya guda wacce ta kunshi batutuwan da dama da suka shafi yankin.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi kira ga sojoji, ‘yan sanda, da jami’an tattara bayanan sirri, da su tabbata an kubutar da dukkan daliban da aka yi garkuwa da su, tare da tabbatar da cewa an ceto su cikin koshin lafiya.
Kazalika gwamnonin sun kara jaddada matsayarsu ta cewa Najeriya ta ci gaba da zama a matsayin kasa dunkulalliya bisa tsari na adalci.
“A irin duniyar da nake rayuwa, idan ka ce sai da safe, ba ka sake komawa ka ce ina wuni." In ji Obasanjo.
Yankin garin Zaria a ‘yan kwanakin nan yana yawan fadawa tarkon ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane don neman kudin fansa.
Dubban mutane ne ke zaune a sansanin ‘yan gudun hijira da ke kananan hukumomin Kukawa, Marte, Bama, Gwoza da Ngala.
Shugaban Najeriya ya yi kira ga daukacin ‘yan kasar da sauran al’umar duniya da su taya Paparoma da addu’a.
A ‘yan kwanakin nan an yi ta tafka muharawa a Najeriya musamman daga bangaren ‘yan adawa kan cewa gwamnatin Buhari tana cin bashin da ya wuce kima.
Rundunar ‘yan sandan jihar Legas da ke Kudu maso yammacin Najeriya ta musanta rahotannin da ke cewa wata matashiya ta mutu sanadiyyar harbin da suka yi don tarwatsa masu zanga-zangar kafa kasar Yarbawa.
Rahotanni sun ce Sunday Igboho da jami'an tsaro ke nema ruwa a jallo, bai halarci gangamin ba.
Kwantiragin Lionel Messi a Barcelona ya kare a ranar 30 ga watan Yuni, abin da ke nufin dan wasan wanda dan asalin kasar Argentina ne na zaman kansa kenan.
Domin Kari