Dan wasan Jamhuriyar Tsakiyar Afirka Karl Namnganda ne ya zura kwallo a ragar Najeriya a minti na karshe a wasan wanda aka buga a ranar Alhamis a birnin Lagos da ke kudancin Najeriya.
Sakataren jam’iyyar na kasa Mr. Kola Ologbondiyan ne ya fadawa manema labarai wannan matsaya da aka cimma bayan taron kwamitin zartawar jam’iyyar na kasa da aka yi a Abuja a ranar Alhamis.
Dan shekara 23, Aryan Khan, shi ne babban dan Shah Rukh Khan, fitaccen jarumi a masana'antar shirya fina-finai ta Bollywood a India.
A ranar Laraba Malami ya fadawa manema labarai cewa mai yiwuwa a saka dokar ta-baci a jihar ta Anambra saboda karin tabarbarewar tsaro da ake gani a yankin.
Tun bayan da aka ba da belin Faisal Maina a watan Nuwambar 2019 ya daina bayyana a gaban kotun yayin da ake ci gaba da sauraren kararsa.
Hukumar zabe ta INEC ta nuna damuwa kan rashin cikakken tsaro a yankin yayin da take shirin tura ma’aikatan da za su gudanar da zaben.
A ranar 6 ga watan Nuwamba hukumar INEC take shirin gudanar da zaben gwamna a jihar ta Anambra wacce ke kudu maso gabashin Najeriya.
Duk da cewa ya gyara matsalar, Facebook bai bayyana takamaiman abin da ya haifar da katsewar ba.
Gabanin kalaman na Mbappe, Darektan wasannin kungiyar Leonardo ya fada cewa yana da kwarin gwiwar dan wasan zai sabunta kwantiraginsa da kungiyar.
A wani sakon Twitter da ya aike, Facebook wanda shi ya mallaki shafukan sada zumantar baki daya ya nemi afuwar masu amfani da su inda ya kara da cewa yana kokarin shawo kan matsalar.
Sai dai kungiyar ta ce ta janye yajin aikin ne iya tsawon mako shida don ta ba gwamnati damar daukan matakan biya mata bukatunta.
A ranar Lahadi Buhari ya isa Addis Ababa, babban birnin kasar ta Habasa don halartar bikin rantsar da Firai Minista Ahmed a wa’adi na biyu.
Ziyarar ta Buhari a Ethiopia na zuwa ne mako guda bayan da ya dawo daga Amurka inda ya halarci taron Majalisar Dinkin Duniya da aka yi a birnin New York.
Sanarwar da fadar shugaban kasar ta fitar ta ce a ranar Talata Buhari zai dawo Abuja.
Manchester United ta raba maki da Everton a wasan da suka buga bayan da aka tashi da ci 1-1 a gasar Premier League ta Ingila.
Blinken ya kara da cewa, Amurka na jinjinawa Najeriya kan irin jagorancin da take yi a nahiyar Afirka wajen samar da zaman lafiya da tsaro.
A farkon watan Satumbar da ya shude hukumomin jihar suka sanar da matakin rufe hanyoyinn sadarwar na wayoyi tare da hadin gwiwar hukumar da ke kula da kamfanonin sadarwa ta NCC a Najeriya.
Messi ya ci kwallon ce a minti na 74 bayan da aka dawo daga hutun rabin lokaci a wasan wanda ya City ta rika rutsa PSG.
Sai dai akwai wadanda suka yi hasashen cewa, Messi zai farfado kuma zai taka rawar gani a sabuwar kungiyar tasa ta PSG yayin da suke shirin karawa da Manchester City.
Domin Kari