Matsalar masu garkuwa da mutane da ke tare hanyar mota ta sa jama’a da dama sun koma tafiya ta jirgin kasa don gujewa fadawa tarkon masu satar mutanen.
Cikin wata sanarwa da ya fitar, Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya taya daukacin al’umar Musulmi murnar zagayowar wannan rana.
Janar Colin Powell, wanda shi ne bakar fata na farko da ya rike mukamin Sakataren harkokin wajen Amurka ya mutu ne a ranar Litinin bayan fama da cutar COVID-19. Shekarunsa 84.
Powell ya rike mukamin sakataren harkokin wajen Amurka a tsakanin shekarun 2001 zuwa 2005 a wa’adin farko na shugaba George W. Bush.
Hukumomin jihar ta Legas sun dora kasuwar baje kolin a ma’aunin kasuwa mafi girma a Najeriya, yammaci da tsakiyar Afirka da ake budewa.
Ita dai Real ta ce a shirye take ta biya fam miliyan 197 don sayen dan wasan dan asalin kasar ta Faransa.
A shekarar 2016 kungiyar IS ta ayyana Al-Barnawi a matasayin shugaban kungiyar ta ISWAP wacce ke kai hare-hare a yankin yammacin Afirka.
Masari ya kara da cewa, akwai lokuta da dama da ake ba da belin ‘yan fashin daji sai su koma su ci gaba da ayyukansu na ta’asa.
A kwanakin baya hukumar zabe ta INEC ta nuna damuwa kan matsalar rashin tsaro da ake fama da ita a jihar, inda ta yi kira ga hukumomi su dauki mataki gabanin zaben.
“Mata shida da yaransu tara suka tsere daga hannun mayakan,” a cewar Kwamishinar mata Zuwaira Gambo.
Akwai alamu da ke nuna cewa mai yiwuwa Rudiger ya ci gaba da zamansa a Stamford Bridge.
Dan wasan Jamhuriyar Tsakiyar Afirka Karl Namnganda ne ya zura kwallo a ragar Najeriya a minti na karshe a wasan wanda aka buga a ranar Alhamis a birnin Lagos da ke kudancin Najeriya.
Sakataren jam’iyyar na kasa Mr. Kola Ologbondiyan ne ya fadawa manema labarai wannan matsaya da aka cimma bayan taron kwamitin zartawar jam’iyyar na kasa da aka yi a Abuja a ranar Alhamis.
Dan shekara 23, Aryan Khan, shi ne babban dan Shah Rukh Khan, fitaccen jarumi a masana'antar shirya fina-finai ta Bollywood a India.
A ranar Laraba Malami ya fadawa manema labarai cewa mai yiwuwa a saka dokar ta-baci a jihar ta Anambra saboda karin tabarbarewar tsaro da ake gani a yankin.
Tun bayan da aka ba da belin Faisal Maina a watan Nuwambar 2019 ya daina bayyana a gaban kotun yayin da ake ci gaba da sauraren kararsa.
Hukumar zabe ta INEC ta nuna damuwa kan rashin cikakken tsaro a yankin yayin da take shirin tura ma’aikatan da za su gudanar da zaben.
A ranar 6 ga watan Nuwamba hukumar INEC take shirin gudanar da zaben gwamna a jihar ta Anambra wacce ke kudu maso gabashin Najeriya.
Duk da cewa ya gyara matsalar, Facebook bai bayyana takamaiman abin da ya haifar da katsewar ba.
Domin Kari