Rundunar ‘yan sanda a jihar Legas ta sanar da cewa ta fara gudanar da bincike kan mutuwar marigayi Sylvester Oromoni, wani dalibin kwalejin Dowen mai shekaru 11 da ake zargin wasu dalibai suka ci zarafinsa har lahira a unguwar Lekki na jihar.
Ministan lafiya, Dakta Osagie Ehanire, ya bayyana rashin jin dadinsa kan yadda gwamnatin Burtaniya ta sanya Najeriya cikin jerin kasashen da ta yiwa lakabi da red list biyo bayan gano nau'in Omicron na cutar COVID-19.
Farashin Danyen Mai Ya Fadi Kasa da Dala 70 Yayin da Haramcin Balaguro ke Barazana Faruwa Sakamakon Nau’in Omicron na cutar coronavirus.
Kamfanin jiragen sama na Emirates zai ci gaba da aikin jigilar fasinjoji tsakanin Dubai da Najeriya daga ranar 5 ga watan Disamban da mu ke ciki.
"An kori malaman ne bayan gudanar da bincike a makarantu, jami’o’i da kwalejojin da suka ce sun yi karatu, inda aka gano cewa sun gabatar da takardun bogi ne ba su yi karatu a inda suka ce sun yi ba."
Mai shari’a Binta Nyako ta babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta gabatar da shari’ar da ake yi wa shugaban kungiyar IPOB mai fafutukar kafa kasar Biyafra, Nnamdi Kanu, inda ta sauya ranar shari’ar daga ranar 19 zuwa 18 ga watan Janairun shekarar 2022.
Fasinjoji a tashar jiragen kasa a Kaduna na ci gaba da kokawa kan yadda wasu mutane da ake zargin ba ma’aikatan hukumar NRC ne ba ke saran tikiti tare da saidawa da tsada kama daga naira dubu bakwai.
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce kamfanin Twitter ya amince da dukkan sharuddan da ta gindaya na gudanar da ayyukansa a kasar.
A yayin da ake dakon farar takardar rahoton kwamitin duba zargin kashe masu zanga-zangar ENDSARS a Lekki, karamin ministan kwadago, Festus Keyamo, ya caccaki kwamitin da aka kafa domin binciken laifukan cin zarafi da kisan gilla da ake yiwa 'yan sanda a zanga-zangar ENDSARS.
Hukumar kula da cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta ce tana sa ido kan bayanan da ke fitowa kan sabon nau'in cutar COVID-19 na Omicron, wanda aka fara ganowa kwanan nan a kasar Afirka ta kudu.
Jam’iyyar APC mai mulki ta sanar da cewa a watan Fabrairun 2022 za a yi babban taronta na kasa.
Kungiyar matan shuwagabannin kasashen nahiyar Afrika kan zaman lafiya ta gudanar da taron yini guda karo na 9 wanda uwargidan shugaban Najeriya Aisha Muhammadu Buhari ta karbi bakuncinsa a wannan karon a birnin tarayyar kasar Abuja.
Jihar Kano ta tara makudan kudaden shiga a matsayin haraji wato VAT fiye da daukacin shiyyar Kudu maso Gabas a cikin watanni takwas na farkon shekarar 2021 kamar yadda wata takarda ta hukumar FIRS ta tabbatar.
Wani Dillalin Miyagun Kwayoyi Da Ya Boye Hodar Ibilis A Ban Dakin Filin Tashi Da Saukan Jiragen Saman Legas Ya Shiga Hannu
‘Yan bindiga da ba a iya tantance iya adadinsu ba sun koma tare hanyar Abuja zuwa Kaduna inda suka afka wa matafiya tare da harbe wani tsohon dan takarar gwamna a jihar Zamfara, Alhaji Sagiru Hamidu, tare da sace wasu da dama.
Har yanzu tsuguni ba ta kare ba a game da batun neman mafita kan halin tsaro da yanayin da makarantun yankin arewacin Najeriya ke ciki.
Fitaccen marubuci kuma mai karantarwa a Najeriya, Mal. Khalid Abdullahi Zaria ya ce kusan kullum ana yin musu a kan abubuwan da suka shafi tarihi a kasar, kama daga kaka da kakanni, addini, zuwan bayajidda da dai sauransu.
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta karbi takardar neman shiga tsarin samun gida guda dubu 7 da 315 na tsarin gidajenta guda dubu 5 da aka gina a karkashin shirin gidaje na kasa mako daya da kaddamar da aikin.
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce gwamnatin tarayya za ta jiran gwamnatocin jihohi su aiwatar da tsarinsu a game da rahoton ENDSARS, don haka za ta jira sanarwa daga gwamnatocin jihohin kasar da suka kafa kwamitin bincike kan ayyukan cin zarrafin ‘yan sanda a kasar.
Domin Kari