Duk tawagar da ta lashe gasar cin kofin nahiyar Afirka ta 2024 za ta samu kyautar dala miliyan bakwai ($7M), kwatankwacin (Yuro Miliyan 6.4), kamar yadda Hukumar Kwallon Kafar Afirka ta CAF ta bayyana a cikin wata sanarwa a ranar Alhamis.
Ma’aikatar Lafiyar ta ce harin na Isra’ila, ya auku ne a Khan Younis, wanda ke kudancin Gaza, kuma cikin wadanda su ka mutu din har da yara tara.
Shirin Taskar VOA na wannan makon, shiri ne na musanman da Muryar Amurka ta hada a game da yaki ko tashin hankali da ake fama da shi a Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo, da kuma mawuyacin hali da mutane ke ciki sakamakon rikicin.
A cikin watannin 12 da suka gabata, shugabannin Afirka sun ziyarci hedkwatar Tarayyar Turai a Brussels da Indiya da Rasha da Amurka da Saudiyya da Afirka ta Kudu da kuma Turkiyya.
Ruwan sama kamar da bakin kwarya ya haddasa ambaliyar ruwa a tsakiyar Congo da ta yi sanadin mutuwar mutane 22, cikin har wasu iyalan gida daya su 10, kamar yadda wani jami’in yankin ya bayyana a ranar Talata.
“Saboda haka, jita-jitar da ake yadawa cewar zan amfana da sake dawo da yarjejeniya tsakanin Intels da Gwamnatin Tarayya ba gaskiya ba ne, wannan bata suna da kage ne kawai.”
Ana sa ran sabuwar yarjejeniyar za ta kubutar da karin wasu mutane da aka yi garkuwa da su daga Gaza, yayin da Isra’ila za ta saki karin wasu Falasdinawa.
Akalla mutum 573 cikin 11,640 da aka tabbatar sun kamu da cutar a Najeriya sun mutu tun bayan barkewarta a watan Disambar 2022.
Domin Kari