Hare-haren da Isra'ila ta kai a kudancin Gaza cikin dare ya yi sanadiyar mutuwar mutum 22 ciki har da yara kanana 18, jami'an kiwon lafiya suka ce a fada a ranar Lahadi, a daidai lokacin da Amurka ke kokarin neman amincewa da karin biliyoyin daloli na taimakon sojojin Isra'ila, kawarta.